< Deutéronome 16 >

1 Prends garde au mois que les épis mûrissent, et fais la Pâque à l'Eternel ton Dieu; car au mois que les épis mûrissent, l'Eternel ton Dieu t'a fait sortir de nuit hors d'Egypte.
Ku kiyaye watan Abib, ku kuma yi shagalin Bikin Ƙetarewar Ubangiji Allahnku, domin a watan Abib ne ya fitar da ku daga Masar da dad dare.
2 Et sacrifie la Pâque à l'Eternel ton Dieu du gros et du menu bétail, au lieu que l'Eternel aura choisi pour y faire habiter son Nom.
Ku miƙa’yar dabba daga cikin garkenku na tumaki, ko na shanu a matsayin Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji zai zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa.
3 Tu ne mangeras point avec elle de pain levé; tu mangeras avec elle pendant sept jours des pains sans levain, pains d'affliction, parce que tu es sorti en hâte du pays d'Egypte, afin que tous les jours de ta vie tu te souviennes du jour que tu es sorti du pays d'Egypte.
Kada ku ci shi da burodin da aka yi da yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, burodi ne na wahala, gama kun bar Masar da gaggawa, saboda haka dukan kwanakin rayuwarku za ku tuna da lokacin da kuka fita daga Masar.
4 Il ne se verra point de levain chez toi dans toute l'étendue de ton pays pendant sept jours, et on ne gardera rien de la chair du sacrifice que tu auras fait le soir du premier jour, jusqu'au matin.
Kada a iske yisti a cikin mallakarku a dukan ƙasarku har kwana bakwai. Kada ku bar wani nama na hadayar da kuka yi a yammancin ranar farko, yă kwana har safe.
5 Tu ne pourras point sacrifier la Pâque dans tous les lieux de ta demeure que l'Eternel ton Dieu te donne;
Kada ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa a wani garin da Ubangiji Allahnku yake ba ku,
6 Mais [seulement] au lieu que l'Eternel ton Dieu aura choisi pour y faire habiter son Nom; c'est là que tu sacrifieras la Pâque au soir, sitôt que le soleil sera couché, précisément au temps que tu sortis d'Egypte.
sai dai a wurin da ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa. A can za ku miƙa hadayar Bikin Ƙetarewa da yamma, sa’ad da rana tana fāɗuwa, a ranar tunawa da fitowarku daga Masar.
7 Et l'ayant fait cuire, tu la mangeras au lieu que l'Eternel ton Dieu aura choisi; et le matin tu t'en retourneras et t'en iras dans tes tentes.
Ku gasa shi, ku kuma ci a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa. Sa’an nan da safe, ku dawo cikin tentunanku.
8 Pendant six jours tu mangeras des pains sans levain, et au septième jour, qui est l'assemblée solennelle à l'Eternel ton Dieu, tu ne feras aucune œuvre.
Kwana shida za ku ci burodi marar yisti, a rana ta bakwai kuma sai ku yi taro ga Ubangiji Allahnku, a cikin wannan rana ba za ku yi kowane irin aiki ba.
9 Tu te compteras sept semaines; tu commenceras à compter [ces] sept semaines, depuis que tu auras commencé à mettre la faucille en la moisson.
Ku ƙirga makoni bakwai, wato, ku fara ƙirga mako bakwai ɗin daga lokacin da kuka sa lauje don ku yanke hatsinku da suke tsaye.
10 Puis tu feras la fête solennelle des semaines à l'Eternel ton Dieu, en présentant l'offrande volontaire de ta main, laquelle tu donneras, selon que l'Eternel ton Dieu t'aura béni.
Sa’an nan ku yi shagalin Bikin Makoni ga Ubangiji Allahnku, ta wurin ba da hadaya ta yardar rai daidai da albarkun da Ubangiji Allahnku ya yi muku.
11 Et tu te réjouiras en la présence de l'Eternel ton Dieu, toi, ton fils, ta fille, ton serviteur, ta servante, et le Lévite qui est dans tes portes; l'étranger, l'orphelin, et la veuve qui sont parmi toi, au lieu que l'Eternel ton Dieu aura choisi pour y faire habiter son Nom.
Ku kuma yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawan cikin biranenku, har ma da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikinku.
12 Et tu te souviendras que tu as été esclave en Egypte, et tu prendras garde à observer ces statuts.
Ku tuna fa, dā ku bayi ne a Masar, sai ku lura, ku bi waɗannan ƙa’idodi.
13 Tu feras la fête solennelle des Tabernacles pendant sept jours, après que tu auras recueilli [les revenus] de ton aire et de ta cuve.
Ku yi shagalin Bikin Tabanakul har kwana bakwai, bayan kuka gama tattara amfanin gona daga masussukarku da kuma daga wuraren matsin inabinku.
14 Et tu te réjouiras en ta fête solennelle, toi, ton fils, ta fille, ton serviteur et ta servante, le Lévite, l'étranger, l'orphelin, et la veuve qui sont dans tes portes.
Ku yi farin ciki a Bikinku, da ku da’ya’yanku maza da mata, da bayinku maza da mata, da Lawiyawa, da baƙi, da marayu, da kuma gwaurayen da suke zama a cikin biranenku.
15 Tu célébreras pendant sept jours la fête solennelle à l'Eternel ton Dieu, au lieu que l'Eternel aura choisi, quand l'Eternel ton Dieu t'aura béni dans toute ta récolte, et dans tout l'ouvrage de tes mains; et tu seras dans la joie.
Kwana bakwai za ku yi shagalin Bikin ga Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa. Gama Ubangiji Allahnku zai albarkace ku a cikin dukan girbinku da kuma cikin dukan aikin hannuwanku, farin cikinku kuwa zai cika.
16 Trois fois l'an tout mâle d'entre vous se présentera devant l'Eternel ton Dieu, au lieu qu'il aura choisi; [savoir] à la fête solennelle des pains sans levain, et à la fête solennelle des Semaines, et à la fête solennelle des Tabernacles. Mais nul ne se présentera devant la face de l'Eternel à vide.
Sau uku a shekara dukan maza su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da ya zaɓa; a Bikin Burodi Marar Yisti, da a Bikin Makoni, da kuma a Bikin Tabanakul. Babu wani da zai bayyana a gaban Ubangiji hannu wofi.
17 [Mais] chacun donnera à proportion de ce qu'il aura, selon la bénédiction de l'Eternel ton Dieu, laquelle il t'aura donnée.
Dole kowannenku yă kawo kyauta daidai yadda Ubangiji Allahnku ya albarkace shi.
18 Tu t'établiras des juges et des prévôts dans toutes tes villes, lesquelles l'Eternel ton Dieu te donne, selon tes Tribus; afin qu'ils jugent le peuple par un jugement droit.
Ku naɗa alƙalai da shugabanni don kowace kabila, a kowane birnin da Ubangiji Allahnku yake ba ku, za su kuma shari’anta mutane ba nuna bambanci.
19 Tu ne te détourneras point de la justice et tu n'auras point égard à l'apparence des personnes. Tu ne prendras aucun présent; car le présent aveugle les yeux des sages, et corrompt les paroles des justes.
Kada ku ɓata shari’a, ko ku nuna bambanci. Kada ku karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta idanu mai hikima, yă murɗe maganar mai gaskiya.
20 Tu suivras exactement la justice, afin que tu vives, et que tu possèdes le pays que l'Eternel ton Dieu te donne.
Gaskiya ce kaɗai za ku bi don ku rayu, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
21 Tu ne planteras point de bocage, de quelque arbre que ce soit, auprès de l'autel de l'Eternel ton Dieu, lequel tu te seras fait.
Kada ku kafa wani ginshiƙin itacen Ashera kusa da bagaden da kuka gina wa Ubangiji Allahnku,
22 Tu ne te dresseras point non plus de statue; l'Eternel ton Dieu hait ces choses.
kada kuma ku tayar da dutse mai tsarki, gama waɗannan ne Ubangiji Allahnku yana ƙi.

< Deutéronome 16 >