< Daniel 9 >

1 La première année de Darius, fils d'Assuérus, de la race des Mèdes, qui avait été établi Roi sur le Royaume des Caldéens.
A shekara ta fari da mulkin Dariyus ɗan Zerzes (wanda yake Bamediye), wanda aka mai da shi sarki a masarautar Babiloniyawa
2 La première année, [dis-je], de son règne, moi Daniel ayant entendu par les Livres, que le nombre des années, duquel l'Eternel avait parlé au Prophète Jérémie pour finir les désolations de Jérusalem, était de soixante et dix ans;
a shekara ta farko ta mulkinsa, ni, Daniyel na gane daga cikin littattafai, bisa ga maganar Ubangiji da aka faɗa wa annabi Irmiya, cewa zaman Urushalima kango zai kai shekara saba’in.
3 Je tournai ma face vers le Seigneur Dieu, cherchant à faire requête et supplication avec le jeûne, le sac, et la cendre.
Sai na juya wurin Ubangiji Allah na roƙe shi ta wurin addu’a da koke-koke, cikin azumi, ina saye da tsummoki, na kuma zauna a cikin toka.
4 Et je priai l'Eternel mon Dieu, je [lui] fis ma confession, et je dis: Hélas! Seigneur, le [Dieu] Fort, le Grand, le Terrible, qui gardes l'alliance et la miséricorde à ceux qui t'aiment, et qui gardent tes commandements;
Na yi addu’a ga Ubangiji Allahna na furta laifina. “Ya Ubangiji, mai alfarma da kuma Allah mai banrazana, wanda yake cika alkawarinsa na ƙauna ga duk wanda ya ƙaunace shi ya kuma kiyaye dokokinsa,
5 Nous avons péché, nous avons commis l'iniquité, nous avons agi méchamment, nous avons été rebelles, et nous nous sommes détournés de tes commandements et de tes ordonnances;
mun yi zunubi muka kuma yi ba daidai ba. Mu mugaye ne da kuma’yan tawaye; mun juya wa umarninka da shari’unka baya.
6 Et nous n'avons point obéi aux Prophètes tes serviteurs qui ont parlé en ton Nom à nos Rois, à nos principaux, à nos pères, et à tout le peuple du pays.
Ba mu saurari bayinka annabawa ba, waɗanda suka yi magana a sunanka ga sarakunanmu da masu mulkinmu da iyayenmu, da kuma dukan mutanen ƙasa.
7 Ô Seigneur! à toi est la justice, et à nous la confusion de face, qui couvre aujourd'hui les hommes de Juda, et les habitants de Jérusalem, et tous ceux d'Israël qui sont près et qui sont loin, par tous les pays dans lesquels tu les as dispersés, à cause de leur prévarication qu'ils ont commise contre toi.
“Ubangiji, kai mai adalci ne, amma a yau kunya ta rufe mu, mutanen Yahuda da mutanen Urushalima da na dukan Isra’ila, waɗanda suke kusa da kuma nesa, a dukan ƙasashen da ka warwatsa mu saboda rashin amincinmu a gare ka.
8 Seigneur, à nous est la confusion de face, à nos Rois, à nos principaux, et à nos pères, parce que nous avons péché contre toi.
Ya Ubangiji, mu da sarakunanmu, da masu mulkinmu da iyayenmu kunya ta rufe mu saboda mun yi maka zunubi.
9 Les miséricordes et les pardons sont du Seigneur notre Dieu, car nous nous sommes rebellés contre lui.
Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne, mai gafartawa ne kuma, ko da yake mun yi masa tawaye;
10 Et nous n'avons point écouté la voix de l'Eternel notre Dieu pour marcher dans ses lois, qu'il a mises devant nous par le moyen de ses serviteurs, les Prophètes.
ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ba, ba mu kuma kiyaye shari’unsa da ya ba mu ta wuri bayinsa annabawa ba.
11 Et tous ceux d'Israël ont transgressé ta Loi, et se sont détournés pour n'écouter point ta voix; c'est pourquoi l'exécration et le serment écrit dans la Loi de Moïse, serviteur de Dieu, ont fondu sur nous; car nous avons péché contre [Dieu].
Dukan Isra’ila sun karya dokokinka suka kuma juya maka baya, sun ƙi yi maka biyayya. “Saboda haka la’anoni da rantsuwar hukunce-hukuncen da suke a rubuce a cikin Dokar Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi.
12 Et il a ratifié ses paroles qu'il avait prononcées contre nous, et contre nos gouverneurs qui nous ont gouvernés, et il a fait venir sur nous un grand mal, tel qu'il n'en est point arrivé sous tous les cieux de semblable à celui qui est arrivé à Jérusalem.
Ka cika kalmomin da ka yi a kanmu da kuma a kan masu mulkinmu ta wurin kawo mana babban bala’i. A duniya duka ba a taɓa yin wani abu kamar yadda aka yi wa Urushalima ba.
13 Tout ce mal est venu sur nous, selon ce qui est écrit dans la Loi de Moïse; et nous n'avons point supplié l'Eternel notre Dieu, pour nous détourner de nos iniquités, et pour nous rendre attentifs à ta vérité.
Kamar yadda yake a rubuce cikin Dokar Musa, dukan wannan bala’i ya sauko a kanmu, duk da haka ba mu nemi tagomashin Ubangiji Allahnmu ta wurin barin aikatawa zunubanmu, mu kuma mai da hankali a kan gaskiyarka ba.
14 Et l'Eternel a veillé sur le mal, [que nous avons fait] et il l'a fait venir sur nous; car l'Eternel notre Dieu est juste en toutes ses œuvres qu'il a faites, vu que nous n'avons point obéi à sa voix.
Ubangiji bai yi wata-wata wajen kawo mana bala’i ba, domin Ubangiji Allahnmu mai adalci ne a cikin dukan abin da yake yi; duk da haka ba mu yi masa biyayya ba.
15 Or maintenant, Seigneur notre Dieu! qui as tiré ton peuple du pays d'Egypte par main forte, et qui t'es acquis un nom, tel qu'[il paraît] aujourd'hui, nous avons péché, nous avons été méchants.
“Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, wanda ya fito da mutanensa daga Masar ta hannu mai ƙarfi wanda kuma ya yi wa kansa sunan da ya dawwama har yă zuwa yau, mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba.
16 Seigneur, je te prie que selon toutes tes justices ta colère et ton indignation soient détournées de ta ville de Jérusalem, la montagne de ta sainteté; car c'est à cause de nos péchés, et à cause des iniquités de nos pères, que Jérusalem et ton peuple sont en opprobre à tous ceux qui sont autour de nous.
Ya Ubangiji, ta wurin kiyaye dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hukuncinka da ka yi a kan Urushalima, birninka, tudunka mai tsarki. Zunubinmu da laifofin iyayenmu sun mai da Urushalima da kuma mutanenka abin ba’a ga dukan waɗanda suke kewaye da mu.
17 Ecoute donc, maintenant, ô notre Dieu! la requête de ton serviteur, et ses supplications, et pour l'amour du Seigneur fais reluire ta face sur ton Sanctuaire désolé.
“Yanzu, ya Allahnmu, ka ji addu’o’i da koke-koken bayinka. Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka duba da rahama wurinka mai tsarki da ya zama kango.
18 Mon Dieu! prête l'oreille, et écoute; ouvre tes yeux, et regarde nos désolations, et la ville sur laquelle ton Nom a été invoqué; car nous ne présentons point nos supplications devant ta face [appuyés] sur nos justices, mais sur tes grandes compassions.
Ka kasa kunne, ya Allah, ka kuma ji; ka buɗe idanunka ka kuma ga yadda birninka ya zama kango, birnin da yake ɗauke da Sunanka. Ba cewa muna roƙonka saboda mu masu adalci ba ne, amma saboda girman jinƙanka.
19 Seigneur exauce, Seigneur pardonne, Seigneur sois attentif, et opère; ne tarde point, à cause de toi-même, mon Dieu! car ton nom a été invoqué sur ta ville, et sur ton peuple.
Ya Ubangiji, ka saurara! Ya Ubangiji ka gafarta! Ya Ubangiji, ka ji ka kuma yi wani abu! Saboda sunanka, ya Allahna, kada ka yi jinkiri, domin da sunanka ake kiran birninka da jama’arka.”
20 Or comme je parlais encore, et faisais ma requête, et confessais mon péché, et le péché de mon peuple d'Israël, et répandais ma supplication en la présence de l'Eternel mon Dieu, pour la montagne de la sainteté de mon Dieu:
Yayinda da nake magana da addu’a, ina furta zunubina da zunubin mutanena Isra’ila ina miƙa koke-kokena ga Ubangiji Allahna saboda tudunsa mai tsarki,
21 Comme donc je parlais encore dans ma prière, ce personnage Gabriel que j'avais vu en vision du commencement, volant promptement me toucha, environ sur le temps de l'oblation du soir.
yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
22 Il m'instruisit, il me parla, et [me] dit: Daniel, je suis sorti maintenant pour te faire entendre une chose digne d'être entendue.
Ya umarce ni ya kuma ce mini, “Daniyel, yanzu na zo domin in ba ka hikima da ganewa.
23 La parole est sortie dès le commencement de tes supplications, et je suis venu pour te le déclarer, parce que tu es agréable. Entends donc la parole, et entends la vision.
Da zarar ka fara addu’a, an amsa, wadda na zo in faɗa maka, gama ana ƙaunar ka sosai. Saboda haka, ka yi lura da saƙon ka kuma fahimci wahayin.
24 Il y a septante semaines déterminées sur ton peuple, et sur ta sainte ville, pour abolir l'infidélité, consumer le péché, faire propitiation pour l'iniquité, pour amener la justice des siècles, pour mettre le sceau à la vision, et à la prophétie, et pour oindre le Saint des Saints.
“An ƙayyade wa jama’arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa’in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa’an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake haikali.
25 Tu sauras donc, et tu entendras, que depuis la sortie de la parole [portant] qu'on [s'en] retourne, et qu'on rebâtisse Jérusalem, jusqu'au CHRIST le Conducteur, il y a sept semaines et soixante-deux semaines; et les places et la brèche seront rebâties, et cela en un temps d'angoisse.
“Sai ka sani ka kuma fahimci wannan; Tun daga sa’ad da aka kafa doka don a maido a kuma sāke gina Urushalima har sai Shafaffen nan, mai mulki, ya zo, za a yi shekara arba’in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da mafaka.
26 Et après ces soixante-deux semaines, le CHRIST sera retranché, mais non pas pour soi; puis le peuple du Conducteur, qui viendra, détruira la ville et le Sanctuaire, et la fin en sera avec débordement, et les désolations sont déterminées jusqu'à la fin de la guerre.
Bayan shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, za a datse Shafaffen nan zai kuma kasance ba shi da kome. Mutanen mai mulkin za su zo su hallaka birnin da kuma wuri mai tsarki. Ƙarshen zai zo kamar rigyawa. Yaƙi zai ci gaba har ƙarshe, a kuma hallakar kamar yadda aka ƙaddara.
27 Et il confirmera l'alliance à plusieurs dans une semaine, et à la moitié de cette semaine il fera cesser le sacrifice, et l'oblation; puis par le moyen des ailes abominables, qui causeront la désolation, même jusqu'à une consomption déterminée, [la désolation] fondra sur le désolé.
Zai tabbatar da alkawari da mutane masu yawa har na shekara bakwai. A tsakiyar bakwai ɗin nan ɗaya zai kawo ƙarshen duk wata hadaya da baiko. Kuma a kusurwar haikali zai sa abin ƙyama mai kawo hallaka, har sai ƙarshen da aka ƙaddara ya auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”

< Daniel 9 >