< Amos 9 >

1 Je vis le Seigneur se tenant debout sur l'autel, et disant: Frappe le linteau de la porte, et que les poteaux soient ébranlés; et blesse-les tous à la tête, et je tuerai par l'épée ce qui sera resté d'eux; celui d'entre eux qui s'enfuyait ne s'enfuira point; et celui d'entre eux qui échappait, ne réchappera point.
Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
2 Quand ils auraient creusé jusqu'aux lieux les plus bas de la terre, ma main les enlèvera de là; quand ils monteraient jusqu'aux cieux, je les en ferai descendre. (Sheol h7585)
Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
3 Et quand ils se seraient cachés au sommet de Carmel, je les y rechercherai et les enlèverai de là; et quand ils se seraient cachés de devant mes yeux au fond de la mer, je commanderai au serpent de les y mordre.
Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
4 Et lorsqu'ils s'en iront en captivité devant leurs ennemis, je commanderai à l'épée qu'elle les y tue; je mettrai mes yeux sur eux pour leur faire du mal, et non pas pour leur faire du bien.
Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
5 Car c'est le Seigneur l'Eternel des armées qui touche la terre, et elle se fond, et tous ceux qui l'habitent mènent deuil, et elle s'écoule toute comme un fleuve, et est submergée comme par le fleuve d'Egypte.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
6 Qui a bâti ses étages dans les cieux, et qui a établi ses armées sur la terre; qui appelle les eaux de la mer, et qui les répand sur le dessus de la terre; son nom est l'Eternel.
shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
7 Ne m'êtes-vous pas comme les enfants des Cusiens, vous, enfants d'Israël? dit l'Eternel. N'ai-je pas fait monter Israël du pays d'Egypte, et les Philistins de Caphtor, et les Syriens de Kir?
“Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
8 Voici, les yeux du Seigneur l'Eternel sont sur le Royaume pécheur, et je l'abolirai de dessus la terre; mais pourtant je n'abolirai point entièrement la maison de Jacob, dit l'Eternel.
“Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
9 Car voici je commanderai, et je ferai errer la maison d'Israël parmi toutes les nations, comme on fait promener [le grain] dans le crible, sans qu'il en tombe un grain en terre.
“Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
10 Tous les pécheurs de mon peuple mourront par l'épée, eux qui disent: Le mal n'approchera point de nous et ne nous préviendra point.
Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
11 En ce temps-là je relèverai le Tabernacle de David qui sera tombé, et je réparerai ses brèches, et je refermerai ses ouvertures; je le rebâtirai comme [il était] aux jours anciens.
“A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
12 Afin qu'ils possèdent le reste de l'Idumée, et toutes les nations sur lesquelles mon Nom sera invoqué; dit l'Eternel, qui fait cela.
domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
13 Voici, les jours viennent, dit l'Eternel, que le laboureur atteindra le moissonneur, et que celui qui foule les raisins atteindra celui qui jette la semence; et les montagnes distilleront le moût, et tous les coteaux en découleront.
“Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
14 Et je ramènerai de la captivité ceux de mon peuple d'Israël qui auront été emmenés captifs, et on rebâtira les villes désertes, et on y habitera; ils planteront des vignes, et ils en boiront le vin; ils feront aussi des jardins, et ils en mangeront les fruits.
Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
15 Je les planterai sur leur terre, et ils ne seront plus arrachés de leur terre, laquelle je leur ai donnée; dit l'Eternel ton Dieu.
Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.

< Amos 9 >