< Actes 4 >

1 Mais comme ils parlaient au peuple, les Sacrificateurs, et le Capitaine du Temple, et les Sadducéens, survinrent.
Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
2 Etant en grande peine de ce qu'ils enseignaient le peuple, et qu'ils annonçaient la résurrection des morts au Nom de Jésus.
Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
3 Et les ayant fait arrêter, ils les mirent en prison jusqu'au lendemain, parce qu'il était déjà tard.
Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
4 Et plusieurs de ceux qui avaient ouï la parole, crurent; et le nombre des personnes fut d'environ cinq mille.
Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
5 Or il arriva que le lendemain leurs Gouverneurs, les Anciens et les Scribes s'assemblèrent à Jérusalem;
Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
6 Avec Anne souverain Sacrificateur, et Caïphe, et Jean, et Alexandre, et tous ceux qui étaient de la race Sacerdotale.
Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
7 Et ayant fait comparaître devant eux Pierre et Jean, ils leur demandèrent: par quelle puissance, ou au Nom de qui avez-vous fait cette [guérison]?
Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
8 Alors Pierre étant rempli du Saint-Esprit, leur dit: Gouverneurs du peuple, et vous Anciens d'Israël:
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
9 Puisque nous sommes recherchés aujourd'hui pour un bien qui a été fait en la personne d'un impotent, pour savoir comment il a été guéri;
In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
10 Sachez vous tous et tout le peuple d'Israël, que ç'a été au Nom de Jésus-Christ le Nazarien, que vous avez crucifié, [et] que Dieu a ressuscité des morts; c'est, [dis-je], en son Nom, que cet homme qui parait ici devant vous, a été guéri.
to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
11 C'est cette Pierre, rejetée par vous qui bâtissez, qui a été faite la pierre angulaire.
Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
12 Et il n'y a point de salut en aucun autre: car aussi il n'y a point sous le ciel d'autre Nom qui soit donné aux hommes par lequel il nous faille être sauvés.
Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
13 Eux voyant la hardiesse de Pierre et de Jean, et sachant aussi qu'ils étaient des hommes sans lettres, et idiots, s'en étonnaient, et ils reconnaissaient bien qu'ils avaient été avec Jésus.
Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
14 Et voyant que l'homme qui avait été guéri, était présent avec eux, ils ne pouvaient contredire en rien.
Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
15 Alors leur ayant commandé de sortir hors du Conseil, ils conféraient entre eux,
Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
16 Disant: que ferons-nous à ces gens? car il est connu à tous les habitants de Jérusalem, qu'un miracle a été fait par eux, et cela est si évident, que nous ne le pouvons nier.
Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
17 Mais afin qu'il ne soit plus divulgué parmi le peuple, défendons-leur avec menaces expresses, qu'ils n'aient plus à parler en ce Nom à qui que ce soit.
Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
18 Les ayant donc appelés, ils leur commandèrent de ne parler plus ni d'enseigner en aucune manière au Nom de Jésus.
Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
19 Mais Pierre et Jean répondant, leur dirent: jugez s'il est juste devant Dieu de vous obéir plutôt qu'à Dieu.
Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
20 Car nous ne pouvons que nous ne disions les choses que nous avons vues et ouies.
Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
21 Alors ils les relâchèrent avec menaces, ne trouvant point comment ils les pourraient punir, à cause du peuple, parce que tous glorifiaient Dieu de ce qui avait été fait.
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 Car l'homme en qui avait été faite cette miraculeuse guérison avait plus de quarante ans.
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
23 Or après qu'on les eut laissés aller, ils vinrent vers les leurs, et leur racontèrent tout ce que les principaux Sacrificateurs et les Anciens leur avaient dit.
Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
24 Ce qu'ayant entendu, ils élevèrent tous ensemble la voix à Dieu, et dirent: Seigneur! tu es le Dieu qui as fait le ciel et la terre, la mer, et toutes les choses qui y sont;
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
25 Et qui as dit par la bouche de David ton serviteur: pourquoi se sont émues les Nations, et les peuples ont-ils projeté des choses vaines?
Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
26 Les Rois de la terre se sont trouvés en personne, et les Princes se sont joints ensemble contre le Seigneur, et contre son Christ.
Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
27 En effet, contre ton saint Fils Jésus, que tu as oint, se sont assemblés Hérode et Ponce Pilate, avec les Gentils, et les peuples d'Israël,
Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
28 Pour faire toutes les choses que ta main et ton conseil avaient auparavant déterminé qui seraient faites.
Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
29 Maintenant donc, Seigneur, fais attention à leurs menaces, et donne à tes serviteurs d'annoncer ta parole avec toute hardiesse;
Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
30 En étendant ta main afin qu'il se fasse des guérisons, et des prodiges, et des merveilles, par le Nom de ton saint Fils Jésus.
Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 Et quand ils eurent prié, le lieu où ils étaient assemblés trembla; et ils furent tous remplis du Saint-Esprit, et ils annonçaient la parole de Dieu avec hardiesse.
Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
32 Or la multitude de ceux qui croyaient, n'était qu'un cœur et qu'une âme; et nul ne disait d'aucune des choses qu'il possédait, qu'elle fût à lui; mais toutes choses étaient communes entre eux.
Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
33 Aussi les Apôtres rendaient témoignage avec une grande force à la résurrection du Seigneur Jésus; et une grande grâce était sur eux tous.
Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
34 Car il n'y avait entre eux aucune personne nécessiteuse; parce que tous ceux qui possédaient des champs ou des maisons, les vendaient, et ils apportaient le prix des choses vendues;
Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
35 Et le mettaient aux pieds des Apôtres; et il était distribué à chacun selon qu'il en avait besoin.
su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
36 Or Joses, qui par les Apôtres fut surnommé Barnabas, c'est-à-dire, fils de consolation, Lévite, et Cyprien de nation,
Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
37 Ayant une possession, la vendit, et en apporta le prix, et le mit aux pieds des Apôtres.
ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.

< Actes 4 >