< 2 Samuel 20 >

1 Et il se trouva là un méchant homme qui avait nom Sébah, fils de Bicri, homme de Jémini, qui sonna de la trompette, et qui dit: Nous n'avons point de part avec David, ni d'héritage [à attendre du] fils d'Isaï. Ô Israël! que chacun [se retire] en ses tentes.
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 Ainsi tous les hommes d'Israël se séparèrent de David, et suivirent Sébah fils de Bicri; mais les hommes de Juda s'attachèrent à leur Roi, [et l'accompagnèrent] depuis le Jourdain jusqu'à Jérusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 Or quand David fut venu en sa maison à Jérusalem, il prit ses dix femmes concubines qu'il avait laissées pour garder sa maison, et les fit garder dans une maison, [où il] les nourrissait; mais il n'allait point vers elles; ainsi elles furent séquestrées jusqu'au jour de leur mort, pour vivre en veuvage.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Puis le Roi dit à Hamasa: Assemble-moi dans trois jours à cri public les hommes de Juda, et représente toi ici.
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 Hamasa donc s'en alla assembler à cri public ceux de Juda; mais il tarda au delà du temps qu'on lui avait assigné.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 Et David dit à Abisaï: Maintenant Sébah fils de Bicri nous fera plus de mal que n'a fait Absalom; toi [donc] prends les serviteurs de ton Seigneur, et le poursuis, de peur qu'il ne trouve quelques villes fortes, et que nous ne le perdions de vue.
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 Ainsi les gens de Joab sortirent après lui, avec les Kéréthiens, et les Péléthiens, et tous les hommes forts; ils sortirent donc de Jérusalem pour poursuivre Sébah fils de Bicri.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 Et comme ils étaient auprès de la grande pierre qui est à Gabaon, Hamasa vint au devant d'eux, et Joab avait sa casaque, dont il était vêtu, ceinte, et son épée était ceinte par dessus, attachée sur ses reins dans son fourreau, et quand il sortit elle tomba.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Et Joab dit à Hamasa: Te portes-tu bien, mon frère? Puis Joab prit de sa main droite la barbe de Hamasa pour le baiser.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 Or Hamasa ne prenait point garde à l'épée qui était en la main de Joab; et Joab l'en frappa à la cinquième côte, et répandit ses entrailles à terre, sans le frapper une seconde fois; et ainsi il mourut. Après cela Joab et Abisaï son frère poursuivirent Sébah fils de Bicri.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 Alors un des serviteurs de Joab s'arrêta auprès d'Hamasa, et dit: Quiconque aime Joab, et quiconque est pour David, qu'il suive Joab.
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 Et Hamasa était vautré dans son sang au milieu du chemin; mais cet homme-là voyant que tout le peuple s'arrêtait, poussa Hamasa hors du chemin dans un champ, et jeta un vêtement sur lui, après qu'il eut vu que tous ceux qui venaient à lui s'arrêtaient.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 Et quand on l'eut ôté du chemin, tous les hommes qui suivaient Joab passaient au delà, afin de poursuivre Sébah fils de Bicri;
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Qui passa par toutes les Tribus d'Israël, jusqu'à Abelah, et Beth-mahaca, avec tous les Bériens qui s'étaient assemblés, et qui aussi l'avaient suivi.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 Les gens donc de Joab s'en vinrent, et l'assiégèrent à Abel Beth-mahaca, et ils élevèrent une terrasse contre la ville, au devant de la muraille; et tout le peuple qui était avec Joab rompait la muraille pour la faire tomber.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 Alors une femme sage de la ville s'écria: Ecoutez, écoutez: Dites, je vous prie, à Joab: Approche-toi d'ici, [et] que je parle à toi.
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 Et quand il se fut approché d'elle, elle lui dit: Es-tu Joab? Il répondit: Je le suis. Elle lui dit: Ecoute les paroles de ta servante. Il répondit: J'écoute.
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 Elle parla encore, et dit: On disait communément autrefois: Qu'on aille demander conseil à Abel, et on a ainsi continué.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 Entre les [villes] fidèles d'Israël je suis une des plus paisibles; tu cherches à détruire une ville qui est une des capitales d'Israël; pourquoi détruirais-tu l'héritage de l'Eternel?
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 Joab lui répondit, et dit: A Dieu ne plaise! à Dieu ne plaise que je détruise, ni que je ruine!
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 La chose n'est pas ainsi; mais un homme de la montagne d'Ephraïm, qui a nom Sébah, fils de Bicri, a levé sa main contre le Roi David; livrez-le moi lui seul, et je m'en irai de devant la ville. Et la femme dit à Joab: Voici, sa tête te sera jetée de dessus la muraille.
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Cette femme-là donc vint vers tout le peuple, et leur parla sagement, et ils coupèrent la tête à Sébah fils de Bicri, et la jetèrent à Joab. Alors on sonna de la trompette, et chacun se retira de devant la ville en sa tente; puis Joab s'en retourna vers le Roi à Jérusalem.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Joab donc [demeura établi] sur toute l'armée d'Israël, et Bénaja fils de Jéhojadah sur les Kéréthiens, et sur les Péléthiens;
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 Et Adoram sur les tributs, et Jehosaphat fils d'Ahilud était commis sur les Registres.
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 Séla était le Secrétaire; et Tsadok et Abiathar étaient les Sacrificateurs.
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 Et Hira Jaïrite était le principal officier de David.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.

< 2 Samuel 20 >