< 2 Samuel 15 >

1 Or il arriva après cela qu'Absalom se pourvut de chariots, et de chevaux; et il avait cinquante archers qui marchaient devant lui.
Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
2 Et Absalom se levait le matin, et se tenait à côté du chemin qui allait vers la porte; et s'il y avait quelqu'un qui eût quelque affaire, pour laquelle il fallût aller vers le Roi afin de demander justice, Absalom l'appelait, et lui disait: De quelle ville es-tu? et il répondait: Ton serviteur est d'une telle Tribu d'Israël.
Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
3 Et Absalom lui disait: Regarde, ta cause est bonne et droite; mais tu n'as personne qui [ait ordre du] Roi de t'entendre.
Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
4 Absalom disait encore: Oh! que ne m'établit-on pour juge dans le pays! et tout homme qui aurait des procès, et qui aurait droit, viendrait vers moi, et je lui ferais justice.
Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
5 Il arrivait aussi que quand quelqu'un s'approchait de lui pour se prosterner devant lui, il lui tendait sa main, et le prenait, et le baisait.
Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
6 Absalom en faisait ainsi à tous ceux d'Israël qui venaient vers le Roi pour avoir justice; et Absalom gagnait les cœurs de ceux d'Israël.
Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
7 Et il arriva au bout de quarante ans, qu'Absalom dit au Roi: Je te prie que je m'en aille à Hébron pour m'acquitter de mon vœu que j'ai voué à l'Eternel.
A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
8 Car quand ton serviteur demeurait à Guesur en Syrie, il fit un vœu, en disant: Si l'Eternel me ramène pour être en repos à Jérusalem, j'en témoignerai ma reconnaissance à l'Eternel.
Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
9 Et le Roi lui répondit: Va en paix. Il se leva donc et s'en alla à Hébron.
Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
10 Or Absalom avait envoyé dans toutes les Tribus d'Israël des gens apostés, pour dire: Aussitôt que vous aurez entendu le son de la trompette, dites: Absalom est établi Roi à Hébron.
Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
11 Et deux cents hommes de Jérusalem qui avaient été invités, s'en allèrent avec Absalom, et ils y allaient dans la simplicité [de leur cœur], ne sachant rien de [cette affaire].
Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
12 Absalom envoya aussi appeler, quand il offrait ses sacrifices, Achithophel Guilonite, conseiller de David, de sa ville de Guilo; et la conjuration devint plus puissante, parce que le peuple allait en augmentant avec Absalom.
Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
13 Alors il vint à David un messager, qui lui dit: Tous ceux d'Israël ont leur cœur tourné vers Absalom.
Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
14 Et David dit à tous ses serviteurs qui étaient avec lui à Jérusalem: Levez-vous, et fuyons; car nous ne saurions échapper devant Absalom. Hâtez-vous d'aller, de peur qu'il ne se hâte, qu'il ne nous atteigne, qu'il ne fasse venir le mal sur nous, et qu'il ne frappe la ville au tranchant de l'épée.
Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
15 Et les serviteurs du Roi répondirent au Roi: Tes serviteurs sont prêts à faire tout ce que le Roi notre Seigneur trouvera bon.
Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
16 Le Roi donc sortit, et toute sa maison le suivait; mais le Roi laissa dix femmes, [qui étaient ses] concubines, pour garder la maison.
Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
17 Le Roi donc sortit, et tout le peuple le suivait; et ils s'arrêtèrent en un lieu éloigné.
Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
18 Et tous ses serviteurs marchaient à côté de lui; et tous les Kéréthiens, et tous les Péléthiens, et tous les Guittiens, [qui étaient] six cents hommes venus de Gath, pour être à sa suite, marchaient devant le Roi.
Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
19 Mais le Roi dit à Ittaï, Guittien: Pourquoi viendrais-tu aussi avec nous? retourne-t'en, et demeure avec le Roi; car tu es étranger, et même tu vas retourner [bientôt] en ton lieu.
Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
20 Tu ne fais que de venir; et te ferais-je aujourd'hui aller errant çà et là avec nous? car quant à moi, je m'en vais où je pourrai; retourne-t'en et remène tes frères; que la gratuité et la vérité soient avec toi.
Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
21 Mais Ittaï répondit au Roi, en disant: L'Eternel est vivant, et le Roi mon Seigneur vit, qu'en quelque lieu où le Roi mon Seigneur sera, soit à la mort, soit à la vie, ton serviteur y sera aussi.
Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
22 David donc dit à Ittaï: Viens, et marche. Alors Ittaï Guittien marcha avec tous ses gens, et tous ses petits enfants qui étaient avec lui.
Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
23 Et tout le pays pleurait à grands cris, et tout le peuple passait plus avant; puis le Roi passa le torrent de Cédron, et tout le peuple passa vis-à-vis du chemin tirant vers le désert;
Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
24 Là aussi était Tsadok avec tous les Lévites qui portaient l'Arche de l'alliance de Dieu, et ils posèrent [là] l'Arche de Dieu; et Abiathar monta pendant que tout le peuple achevait de sortir de la ville.
Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
25 Et le Roi dit à Tsadok: Reporte l'Arche de Dieu dans la ville; si j'ai trouvé grâce devant l'Eternel il me ramènera, et me la fera voir, avec son Tabernacle.
Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
26 Que s'il me dit ainsi: Je ne prends point de plaisir en toi; me voici, qu'il fasse de moi ce qu'il lui semblera bon.
Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
27 Le Roi dit encore au Sacrificateur Tsadok: N'es-tu pas le Voyant? retourne-t'en en paix à la ville, et Ahimahats ton fils, et Jonathan fils d'Abiathar, vos deux fils avec vous.
Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
28 Regardez, je m'en vais demeurer dans les campagnes du désert, jusqu'à ce qu'on vienne m'apporter des nouvelles de votre part.
Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
29 Tsadok donc et Abiathar reportèrent l'Arche de Dieu à Jérusalem, et demeurèrent là.
Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
30 Et David montait par la montée des oliviers, et en montant il pleurait, et il avait la tête couverte, et marchait nu-pieds; tout le peuple aussi qui était avec lui, montait chacun ayant sa tête couverte, et en montant ils pleuraient.
Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
31 Alors on fit ce rapport à David, et on lui dit: Achithophel est parmi ceux qui ont conjuré avec Absalom. Et David dit: Je te prie, ô Eternel! assoli le conseil d'Achithophel.
To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
32 Et il arriva que quand David fut venu jusqu'au sommet [de la montagne], là où il se prosterna devant Dieu, voici Cusaï Arkite, vint au devant de lui, ayant ses habits déchirés, et de la terre sur sa tête.
Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
33 Et David lui dit: Tu me seras à charge, si tu passes plus avant avec moi.
Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
34 Mais si tu t'en retournes à la ville, et si tu dis à Absalom: Ô Roi! je serai ton serviteur, et comme j'ai été dès longtemps serviteur de ton père, je serai maintenant ton serviteur, tu dissiperas le conseil d'Achithophel.
Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
35 Et les Sacrificateurs Tsadok et Abiathar ne seront-ils pas là avec toi? de sorte que tout ce que tu auras entendu de la maison du Roi, tu le rapporteras aux Sacrificateurs Tsadok et Abiathar.
Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
36 Voici leurs deux fils, Ahimahats [fils] de Tsadok, et Jonathan [fils] d'Abiathar, sont là avec eux; vous m'apprendrez par eux tout ce que vous aurez entendu.
’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
37 Ainsi Cusaï l'intime ami de David retourna dans la ville, et Absalom vint à Jérusalem.
Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.

< 2 Samuel 15 >