< 2 Rois 6 >

1 Or les fils des Prophètes dirent à Elisée: Voici maintenant, le lieu où nous sommes assis devant toi, est trop étroit pour nous.
Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
2 Allons-nous-en maintenant jusqu'au Jourdain, et nous prendrons de là chacun de nous une pièce de bois, et nous ferons là un lieu pour y demeurer; et il répondit: Allez.
Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
3 Et l'un d'eux dit: Je te prie qu'il te plaise de venir avec tes serviteurs; et il répondit: J'y irai.
Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
4 Il s'en alla donc avec eux; et ils allèrent au Jourdain, et ils coupèrent du bois.
Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
5 Mais il arriva que comme l'un d'eux abattait une pièce de bois, le fer [de sa cognée] tomba dans l'eau; et il s'écria, et dit: Hélas mon Seigneur! encore est-il emprunté.
Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
6 Et l'homme de Dieu dit: Où est-il tombé? et il lui montra l'endroit; alors [Elisée] coupa un morceau de bois, et le jeta là, et il fit nager le fer par dessus.
Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
7 Et il dit: Lève-le; et [cet homme] étendit sa main, et le prit.
Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
8 Or le Roi de Syrie faisant la guerre à Israël, tenait conseil avec ses serviteurs, et disait: En un tel et un tel lieu sera mon camp.
To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
9 Et l'homme de Dieu envoyait dire au Roi d'Israël: Donne-toi de garde de passer en ce lieu-là, car les Syriens y sont descendus.
Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
10 Et le Roi d'Israël envoyait au lieu que lui disait l'homme de Dieu, et il y pourvoyait, et était sur ses gardes; ce qu'il fit plusieurs fois.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
11 Et le cœur du Roi de Syrie en fut troublé, et il appela ses serviteurs, et leur dit: Ne me découvrirez-vous pas qui est celui des nôtres qui envoie vers le Roi d'Israël?
Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
12 Et l'un de ses serviteurs lui dit: Il n'y en a point, ô Roi mon Seigneur! mais Elisée le Prophète qui est en Israël, déclare au Roi d'Israël les paroles mêmes que tu dis dans la chambre où tu couches.
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
13 Et il dit: Allez, et voyez où il est, afin que j'envoie pour le prendre; et on lui rapporta, en disant: [Le] voilà à Dothan.
Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
14 Et il envoya là des chevaux, et des chariots, et de grandes troupes, qui vinrent de nuit, et qui environnèrent la ville.
Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
15 Or le serviteur de l'homme de Dieu se leva de grand matin, et sortit, et voici des troupes, et des chevaux, et des chariots qui environnaient la ville; et le serviteur de l'homme de Dieu lui dit: Hélas mon Seigneur! comment ferons-nous?
Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
16 Et il lui répondit: Ne crains point; car ceux qui sont avec nous, sont en plus grand nombre que ceux qui sont avec eux.
Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
17 Elisée donc pria, et dit: Je te prie, ô Eternel! ouvre ses yeux, afin qu'il voie; et l'Eternel ouvrit les yeux du serviteur, et il vit, et voici la montagne était pleine de chevaux, et de chariots de feu autour d'Elisée.
Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
18 Puis [les Syriens] descendirent vers Elisée, et il pria l'Eternel, et dit: Je te prie, frappe ces gens d'éblouissement; et Dieu les frappa d'éblouissement, selon la parole d'Elisée.
Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
19 Et Elisée leur dit: Ce n'est pas ici le chemin, et ce n'est pas ici la ville; venez après moi, et je vous mènerai vers l'homme que vous cherchez; et il les mena à Samarie.
Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
20 Et il arriva que sitôt qu'ils furent entrés dans Samarie, Elisée dit: Ô Eternel ouvre leurs yeux afin qu'ils voient. Et l'Eternel ouvrit leurs yeux, et ils virent, et voici ils étaient au milieu de Samarie.
Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
21 Et dès que le Roi d'Israël les eut vus, il dit à Elisée: Frapperai-je, frapperai-je, mon père?
Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
22 Et il répondit: Tu ne frapperas point; frapperais-tu de ton épée et de ton arc ceux que tu aurais pris prisonniers? mets, [au contraire], du pain et de l'eau devant eux, et qu'ils mangent et boivent, et qu'après cela ils s'en aillent vers leur Seigneur.
Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
23 Et il leur fit grand'chère, et ils mangèrent et burent; puis il les laissa aller, et ils s'en allèrent vers leur Seigneur. Depuis ce temps-là les partis de Syrie ne revinrent plus au pays d'Israël.
Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
24 Mais il arriva, après ces choses que Ben-hadad Roi de Syrie, assembla toute son armée, et monta, et assiégea Samarie.
Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
25 Et il y eut une grande famine dans Samarie; car voilà, ils l'assiégèrent si longtemps, que la tête d'un âne se vendait quatre-vingts [pièces] d'argent, et la quatrième partie d'un kad de fiente de pigeons, cinq [pièces] d'argent.
Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
26 Or il arriva que comme le Roi d'Israël passait sur la muraille, une femme lui cria, en disant: Ô Roi mon Seigneur! délivre-moi.
Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
27 Et il répondit: Puisque l'Eternel ne te délivre point, comment te délivrerais-je? Serait-ce de l'aire ou de la cuve?
Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
28 Il lui dit encore: Qu'as-tu? Et elle répondit: Cette femme-là m'a dit: Donne ton fils, et mangeons-le aujourd'hui, et nous mangerons mon fils demain.
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
29 Ainsi nous avons bouilli mon fils, et l'avons mangé, et le jour d'après je lui ai dit: Donne ton fils, et mangeons-le; mais elle a caché son fils.
Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
30 Or dès que le Roi eut entendu les paroles de cette femme, il déchira ses vêtements, (or il passait alors sur la muraille) ce que le peuple vit, et voilà il avait un sac sur sa chair en dedans.
Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
31 C'est pourquoi [le Roi] dit: Dieu me fasse ainsi, et ainsi il y ajoute, si aujourd'hui la tête d'Elisée fils de Saphat demeure sur lui.
Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
32 Et Elisée étant assis dans sa maison, et les Anciens étant assis avec lui, le Roi envoya un homme de sa part; mais avant que le messager fût venu à [Elisée], [Elisée] dit aux Anciens: Ne voyez-vous pas que le fils de ce meurtrier-là a envoyé ici pour m'ôter la tête? Prenez garde, sitôt que le messager sera entré, de fermer la porte, et de l'arrêter à la porte; [n'entendez-vous] pas le bruit des pieds de son maître qui vient après lui?
To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
33 Et comme il parlait encore avec eux, voici le messager descendit vers lui, et [le Roi] dit: Voici, ce mal vient de l'Eternel, qu'attendrai-je plus de l'Eternel?
Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”

< 2 Rois 6 >