< 2 Rois 23 >
1 Alors le Roi envoya, et on assembla vers lui tous les Anciens de Juda et de Jérusalem.
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
2 Et le Roi monta à la maison de l'Eternel, et avec lui tous les hommes de Juda, et tous les habitants de Jérusalem, et les Sacrificateurs et les Prophètes, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu'au plus grand, et on lut, eux l'entendant, toutes les paroles du Livre de l'alliance, qui avait été trouvé dans la maison de l'Eternel.
Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
3 Et le Roi se tint auprès de la colonne, et traita devant l'Eternel cette alliance-ci, qu'ils suivraient l'Eternel, et qu'ils garderaient de tout leur cœur, et de toute leur âme, ses commandements, ses témoignages, et ses statuts, pour persévérer dans les paroles de cette alliance, écrites dans ce Livre; et tout le peuple se tint à cette alliance.
Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
4 Alors le Roi commanda à Hilkija le grand Sacrificateur, et aux Sacrificateurs du second rang, et à ceux qui gardaient les vaisseaux, de tirer hors du Temple de l'Eternel tous les ustensiles qui avaient été faits pour Bahal, et pour les bocages, et pour toute l'armée des cieux; et il les brûla hors de Jérusalem dans les champs de Cédron, et on emporta leur poudre à Béthel.
Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
5 Et il abolit les prêtres des idoles, que les Rois de Juda avaient établis quand on faisait des encensements dans les hauts lieux, dans les villes de Juda, et autour de Jérusalem; il [abolit] aussi ceux qui faisaient des encensements à Bahal; au soleil, à la lune, et aux astres, à toute l'armée des cieux.
Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
6 Il fit aussi emporter le bocage de la maison de l'Eternel hors de Jérusalem, en la vallée de Cédron, et le brûla dans la vallée de Cédron; il le réduisit en poudre, et le jeta sur le sépulcre des enfants du peuple.
Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
7 Ensuite il démolit les maisons des prostitués à paillardise, lesquelles étaient dans la maison de l'Eternel; [et] dans lesquelles les femmes travaillaient à faire des pavillons pour le bocage.
Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
8 Il fit aussi venir des villes de Juda tous les Sacrificateurs, et profana les hauts lieux où les Sacrificateurs avaient fait des encensements, depuis Guébah jusqu'à Béer-sebah; et il démolit les hauts lieux des portes qui étaient à l'entrée de la porte de Josué, capitaine de la ville, laquelle est à la gauche de la porte de la ville.
Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
9 Au reste, ceux qui avaient été Sacrificateurs des hauts lieux ne montaient point vers l'autel de l'Eternel à Jérusalem, mais ils mangeaient des pains sans levain parmi leurs frères.
Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
10 Il profana aussi Topheth, qui était dans la vallée du fils de Hinnom, afin qu'il ne servît plus à personne pour y faire passer son fils ou sa fille par le feu, à Molec.
Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
11 Il ôta aussi de l'entrée de la maison de l'Eternel les chevaux que les Rois de Juda avaient consacrés au soleil, vers le logis de Néthanmélec Eunuque, situé à Parvarim, et il brûla au feu les chariots du soleil.
Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
12 Le Roi démolit aussi les autels qui étaient sur le toit de la chambre haute d'Achaz, que les Rois de Juda avaient faits, et les autels que Manassé avait faits dans les deux parvis de la maison de l'Eternel; il les brisa, les ôtant de là, et il en répandit la poudre au torrent de Cédron.
Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
13 Le Roi profana aussi les hauts lieux qui étaient vis-à-vis de Jérusalem à la main droite sur la montagne des oliviers, [que] Salomon Roi d'Israël avait bâtis à Hastareth, l'abomination des Sidoniens; et à Kémos, l'abomination des Moabites; et à Milkom, l'abomination des enfants de Hammon.
Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
14 Il brisa aussi les statues, et coupa les bocages, et remplit d'ossements d'hommes les lieux ou ils étaient.
Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
15 Il démolit aussi l'autel qui était à Bethel, [et] le haut lieu qu'avait fait Jéroboam fils de Nébat, qui avait fait pécher Israël, cet autel-là, dis-je, et le haut lieu; il brûla le haut lieu, et le réduisit en poudre, et brûla le bocage.
Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
16 Or Josias s'étant tourné, avait vu les sépulcres qui étaient là en la montagne, et il avait envoyé prendre les os des sépulcres, et les avait brûlés sur l'autel, et il l'avait ainsi profané, suivant la parole de l'Eternel, que l'homme de Dieu avait prononcée à haute voix, lorsqu'il prononça ces choses-là à haute voix.
Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
17 Et le Roi avait dit: Qu'est-ce que ce tombeau que je vois? Et les hommes de la ville lui avaient répondu: C'est le sépulcre de l'homme de Dieu qui vint de Juda, et qui prononça à haute voix les choses que tu as faites sur l'autel de Bethel.
Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
18 Et il avait dit: Laissez-le, que personne ne remue ses os; ainsi ils avaient préservé ses os, avec les os du Prophète qui était venu de Samarie.
Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
19 Josias ôta aussi toutes les maisons des hauts lieux qui étaient dans les villes de Samarie, que les Rois d'Israël avaient faites pour irriter [l'Eternel]; et il leur fit selon tout ce qu'il avait fait à Bethel.
Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
20 Et il sacrifia sur les autels tous les sacrificateurs des hauts lieux qui étaient là, et brûla sur eux des ossements d'hommes; puis il s'en retourna à Jérusalem.
Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
21 Alors le Roi commanda à tout le peuple, en disant: Célébrez la Pâque à l'Eternel votre Dieu, en la manière qu'il est écrit au Livre de cette alliance.
Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
22 Et certainement jamais Pâque ne fut célébrée dans le temps des Juges qui avaient jugé en Israël, ni dans tout le temps des Rois d'Israël, et des Rois de Juda,
Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
23 Comme cette Pâque qui fut célébrée en l'honneur de l'Eternel dans Jérusalem, la dix-huitième année du Roi Josias.
Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
24 Josias extermina aussi ceux qui avaient des esprits de Python, les diseurs de bonne aventure, les Théraphims, les dieux de fiente, et toutes les abominations qui avaient été vues dans le pays de Juda, et dans Jérusalem; afin d'accomplir les paroles de la Loi, écrites au livre qu' Hilkija le Sacrificateur avait trouvé dans la maison de l'Eternel.
Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
25 Avant lui il n'y eut point de Roi qui lui fut semblable, qui se retournât vers l'Eternel de tout son cœur, et de toute son âme, et de toute sa force; selon toute la Loi de Moïse; et après lui il ne s'en est point levé de semblable à lui.
Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
26 Toutefois l'Eternel ne revint point de l'ardeur de sa grande colère de laquelle il avait été embrasé contre Juda, à cause de tout ce que Manassé avait fait pour l'irriter.
Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
27 Car l'Eternel avait dit: Je rejetterai aussi Juda de devant ma face, comme j'ai rejeté Israël; et je rejetterai cette ville de Jérusalem, que j'ai choisie, et la maison de laquelle j'ai dit: Mon nom sera là.
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
28 Le reste des faits de Josias, tout ce, dis-je, qu'il a fait, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
29 De son temps, Pharaon-Néco Roi d'Egypte monta contre le Roi des Assyriens vers le fleuve d'Euphrate, et Josias s'en alla au devant de lui, mais dès que Pharaon l'eut vu, il le tua à Méguiddo.
Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
30 Et ses serviteurs le chargèrent mort sur un chariot de Méguiddo, et le portèrent à Jérusalem, et l'ensevelirent dans son sépulcre; et le peuple du pays prit Jéhoachaz, fils de Josias, et ils l'oignirent, et l'établirent Roi en la place de son père.
Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
31 Jéhoachaz était âgé de vingt et trois ans, quand il commença à régner, et il régna trois mois à Jérusalem; sa mère avait nom Hamutal, fille de Jérémie de Libna.
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
32 Il fit ce qui déplaît à l'Eternel, comme avaient fait ses pères.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
33 Et Pharaon-Néco l'emprisonna à Ribla, au pays de Hamath, afin qu'il ne régnât plus à Jérusalem; et il imposa sur le pays une amende de cent talents d'argent, et d'un talent d'or.
Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
34 Puis Pharaon-Néco établit pour Roi Eliakim fils de Josias, en la place de Josias son père, et lui changea son nom, [l'appelant] Jéhojakim; et il prît Jéhoachaz, qui vint en Egypte, où il mourut.
Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
35 Or Jéhojakim donna cet argent et cet or à Pharaon, ayant mis des taxes sur le pays pour fournir cet argent selon le commandement de Pharaon; [et] il leva l'argent et l'or de chacun du peuple du pays selon qu'il était taxé, pour donner à Pharaon-Néco.
Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
36 Jéhojakim était âgé de vingt-cinq ans quand il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem; sa mère avait nom Zebudda, fille de Pédaja de Ruma.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
37 Il fit ce qui déplaît à l'Eternel, comme avaient fait ses pères.
Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.