< 2 Rois 20 >

1 En ce temps-là Ezéchias fut malade à la mort; et le Prophète Esaïe fils d'Amots vint à lui, et lui dit: Ainsi a dit l'Eternel: Dispose de ta maison, car tu t'en vas mourir, et tu ne vivras point.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
2 Alors [Ezéchias] tourna son visage contre la muraille, et fit sa prière à l'Eternel, en disant:
Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
3 Je te prie, ô Eternel! que maintenant tu te souviennes comment j'ai marché devant toi en vérité, et en intégrité de cœur, et comment j'ai fait ce qui t'était agréable. Et Ezéchias pleura abondamment.
“Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 Or il arriva qu'Esaïe n'étant point encore sorti de la cour du milieu, la parole de l'Eternel lui fut adressée, en disant:
Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
5 Retourne, et dis à Ezéchias conducteur de mon peuple: Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu de David ton père; j'ai exaucé ta prière, j'ai vu tes larmes; voici je te vais guérir; dans trois jours tu monteras dans la maison de l'Eternel;
“Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
6 J'ajouterai quinze ans à tes jours, je te délivrerai, toi et cette ville, de la main du Roi des Assyriens; et je garantirai cette ville, pour l'amour de moi, et pour l'amour de David mon serviteur.
Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
7 Puis Esaïe dit: Prenez une masse de figues sèches; et ils la prirent, et la mirent sur l'ulcère; et il fut guéri.
Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
8 Or Ezéchias avait dit à Esaïe: Quel signe aurai-je que l'Eternel me guérira, et qu'au troisième jour je monterai en la maison de l'Eternel?
Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
9 Et Esaïe répondit: Ceci t'est donné par l'Eternel pour un signe que l'Eternel accomplira la parole qu il a prononcée; l'ombre s'avancera-t-elle de dix degrés, ou retournera-t-elle en arrière de dix degrés?
Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
10 Et Ezéchias dit: C'est peu de chose que l'ombre s'avance de dix degrés; non, mais que l'ombre retourne en arrière de dix degrés.
“Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
11 Et Esaïe le Prophète cria à l'Eternel; et l'Eternel fit retourner l'ombre par les degrés par lesquels elle était descendue au cadran d'Achaz, dix degrés en arrière.
Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
12 En ce temps-là Bréodac-Baladan fils de Baladan Roi de Babylone, envoya des Lettres avec un présent à Ezéchias, parce qu'il avait appris qu'Ezéchias avait été malade.
A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
13 Et Ezéchias les ayant entendus leur montra tous ses cabinets les plus curieux, l'argent, et l'or, et les aromates, et ses huiles de senteur, et tout son arsenal, et tout ce qui se trouvait dans ses trésors; il n'y eut rien dans sa maison et dans toute sa cour qu'Ezéchias ne leur montrât.
Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
14 Puis le Prophète Esaïe vint vers le Roi Ezéchias, et lui dit: Qu'ont dit ces gens-là? et d'où sont-ils venus vers toi? Et Ezéchias répondit: Ils sont venus d'un pays fort éloigné, ils sont venus de Babylone.
Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
15 Et [Esaïe] dit: Qu'ont-ils vu dans ta maison? Et Ezéchias répondit: Ils ont vu tout ce qui est dans ma maison; il n'y a rien dans mes trésors que je ne leur aie montré.
Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
16 Alors Esaïe dit à Ezéchias: Ecoute la parole de l'Eternel.
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
17 Voici, les jours viendront que tout ce qui est dans ta maison, et ce que tes pères ont amassé dans leurs trésors jusqu'à ce jour, sera emporté à Babylone; il n'en demeurera rien de reste, a dit l'Eternel.
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
18 On prendra même de tes fils qui seront sortis de toi, [et] que tu auras engendrés, afin qu'ils soient Eunuques au palais du Roi de Babylone.
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
19 Et Ezéchias répondit à Esaïe: La parole de l'Eternel que tu as prononcée, est bonne; et il ajouta: N'y aura-t-il point paix et sûreté pendant mes jours?
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
20 Le reste des faits d'Ezéchias, et tous ses exploits, et comment il fit l'étang, et l'aqueduc par lequel il fit entrer les eaux dans la ville, n'est-il pas écrit au Livre des Chroniques des Rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
21 Et Ezéchias s'endormit avec ses pères; et Manassé son fils régna en sa place.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Rois 20 >