< 2 Rois 18 >
1 Or la troisième année d'Hosée fils d'Ela Roi d'Israël, Ezéchias fils d'Achaz Roi de Juda commença à régner.
A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Il était âgé de vingt-cinq ans quand il commença à régner, et il régna vingt et neuf ans à Jérusalem; sa mère avait nom Abi, [et] était fille de Zacharie.
Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
3 Il fit ce gui est droit devant l'Eternel comme avait fait David son père.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
4 Il ôta les hauts lieux, mit en pièces les statues, coupa les bocages, et il brisa le serpent d'airain que Moïse avait fait, parce que jusqu'à ce jour-là les enfants d'Israël lui faisaient des encensements; et il le nomma Néhustan.
Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
5 Il mit son espérance en l'Eternel le Dieu d'Israël, et après lui il n'y eut point de [Roi] semblable à lui entre tous les Rois de Juda, comme il n'y en avait point eu entre ceux qui avaient été avant lui.
Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
6 Il s'attacha à l'Eternel, il ne s'en détourna point; et il garda les commandements que l'Eternel avait donnés à Moïse.
Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
7 Et l'Eternel fut avec lui partout où il allait, [et] il prospérait; mais il se rebella contre le Roi des Assyriens, pour ne lui être point assujetti.
Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
8 Il frappa les Philistins jusqu'à Gaza, et ses confins, depuis les tours des gardes jusqu'aux villes fortes.
Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
9 Or il arriva en la quatrième année du Roi Ezéchias, qui était la septième du règne d'Hosée fils d'Ela Roi d'Israël, que Salmanéser Roi des Assyriens monta contre Samarie, et l'assiégea.
A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
10 Au bout de trois ans ils la prirent; [et ainsi] la sixième année du règne d'Ezéchias, qui était la neuvième d'Hosée Roi d'Israël, Samarie fut prise.
A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
11 Et le Roi des Assyriens transporta les Israëlites en Assyrie, et les fit mener à Chalach, et sur le Chabor, fleuve de Gozan, et dans les villes des Mèdes;
Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
12 Parce qu'ils n'avaient point obéi à la voix de l'Eternel leur Dieu, mais avaient transgressé son alliance, [et] tout ce que Moïse serviteur de l'Eternel avait commandé; ils n'y avaient point obéi, et ne l'avaient point fait.
Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
13 r en la quatorzième année du Roi Ezéchias, Sanchérib Roi des Assyriens monta contre toutes les villes fortes de Juda, et les prit.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
14 Et Ezéchias Roi de Juda envoya dire au Roi des Assyriens à Lakis: J'ai fait une faute, retire-toi de moi, je payerai tout ce que tu m'imposeras; et le Roi des Assyriens imposa trois cents talents d'argent, et trente talents d'or à Ezéchias Roi de Juda.
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
15 Et Ezéchias donna tout l'argent qui se trouva dans la maison de l'Eternel, et dans les trésors de la maison Royale.
Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
16 En ce temps-là Ezéchias mit en pièces les portes du Temple de l'Eternel, et les linteaux que lui-même avait couverts [de lames d'or], et il les donna au Roi des Assyriens.
A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
17 Puis le Roi des Assyriens envoya de Lakis, Tarta, Rab-saris, et Rab-saké, avec de grandes forces vers le Roi Ezéchias à Jérusalem; et ils montèrent et vinrent à Jérusalem. Or étant montés et venus ils se présentèrent auprès du conduit du haut étang, qui est au grand chemin du champ du foulon.
Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
18 Et ils appelèrent le Roi tout haut. Alors Eliakim fils de Hilkija maître d'hôtel, et Sebna le Secrétaire, et Joach fils d'Asaph, commis sur les Registres, sortirent vers eux.
Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
19 Et Rab-saké leur dit: Dites maintenant à Ezéchias: Ainsi a dit le grand Roi, le Roi des Assyriens: Quelle est cette confiance sur laquelle tu t'appuies?
Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
20 Tu parles, mais ce ne sont que des paroles; le conseil et la force sont requis à la guerre. Mais en qui t'es-tu confié, pour te rebeller contre moi?
Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
21 Voici maintenant, tu t'es confié en l'Egypte, en ce roseau cassé, sur lequel si quelqu'un s'appuie, il lui entrera dans la main, et la percera; tel est Pharaon Roi d'Egypte à tous ceux qui se confient en lui.
Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
22 Que si vous me dites: Nous nous confions en l'Eternel notre Dieu; n'[est]-ce pas celui dont Ezéchias a détruit les hauts lieux, et les autels, et a dit à Juda, et à Jérusalem: Vous vous prosternerez devant cet autel à Jérusalem?
Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
23 Or maintenant donne des otages au Roi des Assyriens mon Maître, et je te donnerai deux mille chevaux, si tu peux donner autant d'hommes pour monter dessus.
“‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
24 Comment donc ferais-tu tourner visage au moindre Gouverneur d'entre les serviteurs de mon Maître? mais tu te confies en l'Egypte, à cause des chariots et des gens de cheval.
Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
25 Mais maintenant suis-je monté sans l'Eternel contre ce lieu-ci pour le détruire? l'Eternel m'a dit: Monte contre ce pays-là, et le détruis.
Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
26 Alors Eliakim fils de Hilkija, et Sebna, et Joach dirent à Rab-saké: Nous te prions de parler en Langue Syriaque à tes serviteurs, car nous l'entendons; et ne nous parle point en Langue Judaïque, le peuple qui est sur la muraille l'écoutant.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
27 Et Rab-saké leur répondit: Mon Maître m'a-t-il envoyé vers ton Maître, ou vers toi, pour parler ce langage? [ne m'a-t-il pas envoyé] vers les hommes qui se tiennent sur la muraille; [pour leur dire] qu'ils mangeront leur propre fiente, et qu'ils boiront leur urine avec vous?
Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
28 Rab-saké donc se tint debout, et s'écria à haute voix en Langue Judaïque, et parla, et dit: Ecoutez la parole du grand Roi, le Roi des Assyriens.
Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
29 Ainsi a dit le Roi: Qu'Ezéchias ne vous abuse point; car il ne vous pourra point délivrer de ma main.
Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
30 Qu'Ezéchias ne vous fasse point confier en l'Eternel, en disant: L'Eternel indubitablement nous délivrera, et cette ville ne sera point livrée entre les mains du Roi des Assyriens.
Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
31 N'écoutez point Ezéchias; car ainsi a dit le Roi des Assyriens: Faites composition avec moi, et sortez vers moi; et vous mangerez chacun de sa vigne, et chacun de son figuier, et vous boirez chacun de l'eau de sa citerne;
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
32 Avant que je vienne, et que je vous emmène en un pays qui est comme votre pays, un pays de froment et de bon vin, un pays de pain et de vignes, un pays d'oliviers qui portent de l'huile, et [un pays] de miel; vous vivrez, et vous ne mourrez point; mais n'écoutez point Ezéchias, quand il vous voudra persuader, en disant: L'Eternel nous délivrera.
har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
33 Les dieux des nations ont-ils délivré chacun leur pays de la main du Roi des Assyriens?
Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
34 Où sont les dieux de Hamath, et d'Arpad; où sont les dieux de Sépharvajim, d'Henah, et de Hiwah? [et] même a-t-on délivré Samarie de ma main?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
35 Qui sont ceux d'entre tous les dieux de ces pays-là qui aient délivré leur pays de ma main, pour dire que l'Eternel délivrera Jérusalem de ma main?
Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
36 Et le peuple se tut, et on ne lui répondit pas un mot; car le Roi avait commandé disant: Vous ne lui répondrez point.
Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
37 Après cela, Eliakim fils de Hilkija Maître d'hôtel, et Sebna le Secrétaire, et Joach fils d'Asaph, commis sur les Registres, s'en revinrent, les vêtements déchirés, vers Ezéchias, et ils lui rapportèrent les paroles de Rab-saké.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.