< 2 Chroniques 35 >
1 Or Josias célébra la Pâque à l'Eternel dans Jérusalem, et on égorgea la Pâque, le quatorzième jour du premier mois.
Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
2 Et il établit les Sacrificateurs en leurs charges, et les encouragea au service de la maison de l'Eternel.
Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
3 Il dit aussi aux Lévites qui enseignaient tout Israël, et qui étaient saints à l'Eternel: Laissez l'Arche sainte au Temple que Salomon fils de David Roi d'Israël a bâti; vous n'avez plus la charge de la porter sur vos épaules, maintenant servez l'Eternel votre Dieu, et son peuple d'Israël;
Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
4 Et rangez-vous selon les maisons de vos pères, selon vos départements, et selon la description qui a été faite par David Roi d'Israël, et la description faite par Salomon son fils.
Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
5 Et aidez vos frères les enfants du peuple, dans le Sanctuaire, selon les départements des maisons des pères, et selon que chaque famille des Lévites est partagée.
“Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
6 Et égorgez la Pâque. Sanctifiez-vous donc, et en apprêtez à vos frères, afin qu'ils la puissent faire selon la parole que l'Eternel a donnée par le moyen de Moïse.
Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
7 Et Josias fit présent à ceux du peuple qui se trouvèrent là, d'un troupeau d'agneaux et de chevreaux, au nombre de trente mille, le tout pour faire la Pâque, et de trois mille bœufs; et ces choses-là étaient des biens du Roi.
Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
8 Ses principaux [officiers] firent aussi de leur bon gré un présent pour le peuple, aux Sacrificateurs et aux Lévites; et Hilkija, Zacharie, et Jéhiël, conducteurs de la maison de Dieu, donnèrent aux Sacrificateurs, pour faire la Pâque, deux mille six cents [agneaux ou chevreaux], et trois cents bœufs.
Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
9 Et Conania, Sémahia, et Nathanaël ses frères, et Hasabia, Jéhiël, et Jozabad, qui étaient les principaux des Lévites, en présentèrent cinq mille aux autres pour faire la Pâque, et cinq cents bœufs.
Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
10 Ainsi le service étant tout préparé, les Sacrificateurs se tinrent en leurs places, et les Lévites en leurs départements, selon le commandement du Roi.
Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
11 Puis on égorgea la Pâque, et les Sacrificateurs répandaient [le sang, le prenant] de leurs mains, et les Lévites écorchaient.
Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
12 Et comme ils les distribuaient selon les départements des maisons des pères de ceux du peuple, ils mirent à part l'holocauste pour l'offrir à l'Eternel, selon qu'il est écrit au Livre de Moïse; et ils en firent ainsi des bœufs.
Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
13 Ils rôtirent donc la Pâque au feu, selon la coutume, mais ils cuisirent dans des chaudières, des chaudrons, et des poêles, les choses consacrées, et les firent courir parmi tout le peuple.
Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
14 Puis ils apprêtèrent [ce qu'il fallait] pour eux, et pour les Sacrificateurs; car les Sacrificateurs, enfants d'Aaron, [avaient été occupés] jusqu'à la nuit en l'oblation des holocaustes et des graisses; c'est pourquoi les Lévites apprêtèrent [ce qu'il fallait] pour eux, et pour les Sacrificateurs, enfants d'Aaron.
Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
15 Et les chantres, enfants d'Asaph, se tinrent en leur place, selon le commandement de David, et d'Asaph, avec [les enfants] d'Héman, et de Jéduthun le Voyant du Roi; les portiers aussi étaient à chaque porte, et il n'était pas besoin qu'ils se détournassent de leur ministère, car les Lévites leurs frères apprêtaient [ce qu'il fallait] pour eux.
Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
16 Et ainsi tout le service de l'Eternel en ce jour-là fut réglé pour faire la Pâque, et pour offrir les holocaustes sur l'autel de l'Eternel, selon le commandement du Roi Josias.
Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
17 Les enfants d'Israël donc qui s'y trouvèrent, célébrèrent la Pâque en ce temps-là, et ils célébrèrent aussi la fête solennelle des pains sans levain pendant sept jours.
Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
18 Or on n'avait point célébré en Israël de Pâque semblable à celle-là, depuis les jours de Samuel le Prophète; et nul des Rois d'Israël n'avait jamais célébré une telle Pâque comme fit Josias, avec les Sacrificateurs et les Lévites, et tout Juda et Israël, qui s'y étaient trouvés avec les habitants de Jérusalem.
Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
19 Cette Pâque fut célébrée la dix-huitième année du règne de Josias.
An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
20 Après tout cela, et après que Josias eut rétabli [l'ordre du Temple], Nécò Roi d'Egypte monta pour faire la guerre à Carkémis sur l'Euphrate; et Josias s'en alla à sa rencontre.
Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
21 Mais [Nécò] envoya vers lui des messagers, pour lui dire: Qu'y a-t-il entre nous, Roi de Juda? Quant à toi, ce n'est pas à toi que j'en veux aujourd'hui, mais à une maison qui me fait la guerre, et Dieu m'a dit que je me hâtasse. Désiste-toi donc de venir contre Dieu, qui est avec moi, afin qu'il ne te détruise.
Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
22 Mais Josias ne voulut point se détourner de lui, mais se déguisa pour combattre contre lui, et il n'écouta point les paroles de Nécò [qui procédaient] de la bouche de Dieu. Il vint donc pour combattre dans la campagne de Méguiddo.
Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
23 Et les archers tirèrent contre le Roi Josias, et le Roi dit à ses serviteurs: Otez-moi d'ici; car on m'a fort blessé.
Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
24 Et ses serviteurs l'ôtèrent du chariot, et le mirent sur un second chariot qu'il avait, et le menèrent à Jérusalem, où il mourut; et il fut enseveli dans les sépulcres de ses pères, et tous ceux de Juda et de Jérusalem menèrent deuil sur Josias.
Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
25 Jérémie aussi fit des lamentations sur Josias, et tous les chanteurs et toutes les chanteuses en parlèrent dans leurs lamentations sur Josias, et ces [lamentations se sont conservées] jusqu'à ce jour, ayant été données en ordonnance à Israël. Or voici ces choses sont écrites dans les lamentations.
Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
26 Et le reste des faits de Josias et ses actions de piété, selon ce qui est écrit dans la Loi de l'Eternel;
Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
27 Ses faits, [dis-je], les premiers et les derniers, voilà ils [sont] écrits au Llivre des Rois d'Israël et de Juda.
dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.