< 2 Chroniques 28 >

1 Achaz était âgé de vingt ans quand il commença à régner, et il régna seize ans à Jérusalem; mais il ne fit point ce qui est droit devant l'Eternel, comme [avait fait] David son père.
Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
2 Mais il suivit le train des Rois d'Israël, et même il fit des images de fonte aux Bahalins.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
3 Il fit aussi des encensements dans la vallée du fils de Hinnom, et fit brûler de ses fils au feu, selon les abominations des nations que l'Eternel avait chassées de devant les enfants d'Israël.
Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 Il sacrifiait aussi et faisait des encensements dans les hauts lieux, et sur les coteaux, et sous tout arbre verdoyant.
Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
5 C'est pourquoi l'Eternel son Dieu le livra entre les mains du Roi de Syrie; tellement que [les Syriens] le défirent, et prirent sur lui un grand nombre de prisonniers, qu'ils emmenèrent à Damas; il fut aussi livré entre les mains du Roi d'Israël, qui fit une grande plaie à [son Royaume].
Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
6 Car Pékach fils de Rémalia tua en un jour six vingt mille hommes de ceux de Juda, tous vaillants hommes, parce qu'ils avaient abandonné l'Eternel le Dieu de leurs pères.
A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
7 Et Zicri, homme puissant d'Ephraïm, tua Mahaséja fils du Roi, et Hazrikam qui avait la conduite de la maison, et Elcana qui tenait le second [rang] après le Roi.
Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
8 Et les enfants d'Israël emmenèrent prisonniers, de leurs frères, deux cent mille personnes, tant femmes, que fils et filles, et ils firent aussi sur eux un gros butin, et ils amenèrent le butin à Samarie.
Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
9 Or il y avait là un Prophète de l'Eternel, nommé Hoded, lequel sortit au devant de cette armée, qui s'en allait entrer à Samarie, et leur dit: Voici, l'Eternel le Dieu de vos pères, étant indigné contre Juda, les a livrés entre vos mains, et vous les avez tués en furie, de sorte que cela est parvenu jusqu'aux cieux.
Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
10 Et maintenant vous faites votre compte de vous assujettir pour serviteurs et pour servantes les enfants de Juda et de Jérusalem; n'est-ce pas vous seuls qui êtes coupables envers l'Eternel votre Dieu?
Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
11 Maintenant donc écoutez-moi, et ramenez les prisonniers que vous avez pris d'entre vos frères; car l'ardeur de la colère de l'Eternel est sur vous.
To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
12 Alors quelques-uns des Chefs des enfants d'Ephraïm, [savoir] Hazaria fils de Jéhohanan, Bérécia fils de Mésillémoth, Ezéchias fils de Sallum, et Hamasa fils de Hadlaï, se levèrent contre ceux qui retournaient de la guerre,
Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
13 Et leur dirent: Vous ne ferez point entrer ici ces prisonniers, car vous prétendez nous rendre coupables devant l'Eternel, en ajoutant ceci à nos péchés et à notre crime, bien que nous soyons très coupables, et que l'ardeur de la colère [de l'Eternel] soit grande sur Israël.
Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
14 Alors les soldats abandonnèrent les prisonniers, et le butin, devant les principaux et toute l'assemblée.
Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
15 Et ces hommes qui ont été [ci-dessus] nommés par leurs noms, se levèrent et prirent les prisonniers, et revêtirent des dépouilles tous ceux d'entr'eux qui étaient nus; et quand ils les eurent vêtus et chaussés, et qu'ils leur eurent donné à manger et à boire, et qu'ils les eurent oints, ils conduisirent sur des ânes tous ceux qui ne se pouvaient pas soutenir, et les amenèrent à Jérico, la ville des palmes, chez leurs frères; puis ils s'en retournèrent à Samarie.
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
16 En ce temps-là le Roi Achaz envoya vers le Roi d'Assyrie, afin qu'il lui donnât du secours.
A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
17 Car outre cela les Iduméens étaient venus, et avaient battu ceux de Juda, et en avaient emmené des prisonniers.
Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
18 Les Philistins aussi s'étaient jetés sur les villes de la campagne, et du Midi de Juda, et avaient pris Beth-sémes, Ajalon, Guédéroth, Soco, et les villes de son ressort, Timna, et les villes de son ressort, et Guimzo, et les villes de son ressort, et ils habitaient là.
yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
19 Car l'Eternel avait abaissé Juda, à cause d'Achaz Roi d'Israël, parce qu'il avait détourné Juda [du service de Dieu], et s'était entièrement adonné à pécher contre l'Eternel.
Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
20 Ainsi Tillegath-Pilnéeser Roi d'Assyrie vint vers lui, mais il l'opprima, bien loin de le fortifier.
Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
21 Car Achaz prit une partie [des trésors] de la maison de l'Eternel, et de la maison Royale, et des principaux [du peuple], et les donna au Roi d'Assyrie; qui cependant ne le secourut point.
Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
22 Et dans le temps qu'on l'affligeait, il continuait toujours à pécher de plus en plus contre l'Eternel; c'était [toujours] le Roi Achaz.
Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
23 Car il sacrifia aux dieux de Damas qui l'avaient battu, et il dit: Puisque les dieux des Rois de Syrie les secourent, je leur sacrifierai, afin qu'ils me secourent aussi; mais ils furent cause de sa chute, et de celle de tout Israël.
Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
24 Et Achaz prit tous les vaisseaux de la maison de Dieu, et les brisa, les vaisseaux, dis-je, de la maison de Dieu, et il ferma les portes de la maison de l'Eternel, et se fit des autels dans tous les coins de Jérusalem.
Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
25 Et il fit des hauts lieux dans chaque ville de Juda, pour faire des encensements à d'autres dieux; et il irrita l'Eternel le Dieu de ses pères.
A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
26 Quant au reste de ses faits, et à toutes ses actions, tant les premières que les dernières, voilà, toutes ces choses sont écrites au Livre des Rois de Juda et d'Israël.
Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Puis Achaz s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit en la Cité, à Jérusalem, mais on ne le mit point dans les sépulcres des Rois d'Israël, et Ezéchias son fils régna en sa place.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chroniques 28 >