< 2 Chroniques 1 >

1 Or Salomon, fils de David, se fortifia dans son règne; et l'Eternel son Dieu fut avec lui, et l'éleva extraordinairement.
Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
2 Et Salomon parla à tout Israël, [savoir] aux Chefs de milliers et de centaines, aux Juges, et à tous les principaux de tout Israël, Chefs des pères.
Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
3 Et Salomon et toute l'assemblée qui était avec lui, allèrent au haut lieu qui était à Gabaon; car là était le Tabernacle d'assignation de Dieu, que Moïse, serviteur de l'Eternel, avait fait au désert.
Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
4 (Mais David avait amené l'Arche de Dieu de Kirjath-jéharim dans le lieu qu'il avait préparé; car il lui avait tendu un Tabernacle à Jérusalem.)
Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
5 Et l'autel d'airain, que Betsaléël, le fils d'Uri, fils de Hur, avait fait, était à [Gabaon], devant le pavillon de l'Eternel, lequel fut aussi recherché par Salomon et par l'assemblée.
Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
6 Et Salomon offrit là devant l'Eternel mille holocaustes sur l'autel d'airain qui était devant le Tabernacle.
Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
7 Cette même nuit Dieu apparut à Salomon, et lui dit: Demande ce que [tu voudras que] je te donne.
A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
8 Et Salomon répondit à Dieu: Tu as usé d'une grande gratuité envers David mon père, et tu m'as établi Roi en sa place.
Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
9 Maintenant [donc], ô Eternel Dieu! que la parole [que tu as donnée] à David mon père soit ferme, car tu m'as établi Roi sur un peuple nombreux, comme la poudre de la terre.
To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
10 Et donne-moi maintenant de la sagesse et de la connaissance, afin que je sorte et que j'entre devant ce peuple; car qui pourrait juger ton peuple, qui est si grand?
Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
11 Et Dieu dit à Salomon: Parce que tu as désiré ces avantages, et que tu n'as point demandé des richesses, ni des biens, ni de la gloire, ni la mort de ceux qui te haïssent, et que tu n'as pas même demandé de vivre longtemps, mais que tu as demandé pour toi de la sagesse et de la connaissance, afin de pouvoir juger mon peuple, sur lequel je t'ai établi Roi;
Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
12 La sagesse et la connaissance te sont données; je te donnerai aussi des richesses, des biens, et de la gloire; ce qui n'est point ainsi arrivé aux Rois qui ont été avant toi, et ce qui n'arrivera [plus] ainsi après toi.
saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
13 Après cela Salomon s'en retourna à Jérusalem du haut lieu qui était à Gabaon, de devant le Tabernacle d'assignation, et il régna sur Israël.
Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
14 Et il fit amas de chariots et de gens de cheval, tellement qu'il avait mille et quatre cents chariots, et douze mille hommes de cheval; et il les mit dans les villes où il tenait ses chariots; il y en eut aussi auprès du Roi à Jérusalem.
Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
15 Et le Roi fit que l'argent et l'or n'étaient non plus prisé dans Jérusalem, que les pierres; et les cèdres, que les figuiers sauvages qui [sont] dans les plaines, tant il y en avait.
Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
16 Or quant au péage qui appartenait à Salomon de la traite des chevaux qu'on tirait d'Egypte, et du fil, les fermiers du Roi se payaient en fil.
Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
17 Mais on faisait monter et sortir d'Egypte chaque chariot pour six cents [pièces] d'argent, et chaque cheval pour cent cinquante; et ainsi on en tirait par le moyen de ces [fermiers] pour tous les Rois des Héthiens, et pour les Rois de Syrie.
Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.

< 2 Chroniques 1 >