< 1 Samuel 3 >
1 Or le jeune garçon Samuel servait l'Eternel en la présence d'Héli; et la parole de l'Eternel était rare en ces jours-là, et il n'y avait point d'apparition de visions.
Yaron nan Sama’ila ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli. A waɗannan kwanaki kuwa jin magana daga wurin Ubangiji ba safai ba, babu kuma wahayi da yawa.
2 Et il arriva un jour, qu'Héli étant couché en son lieu, (or ses yeux commençaient à se ternir, et il ne pouvait voir.)
Wata rana da dare Eli da idanunsa sun kusa makancewa har ba ya iya gani sosai yana kwance a inda ya saba.
3 Et avant que les lampes de Dieu fussent éteintes, Samuel étant aussi couché au Tabernacle de l'Eternel, dans lequel était l'Arche de Dieu;
Fitilar Allah kuwa tana ci, ba tă mutu ba tukuna, Sama’ila kuma na kwance a haikali na Ubangiji inda akwai akwatin Allah.
4 L'Eternel appela Samuel; et il répondit: Me voici.
Sai Ubangiji ya kira Sama’ila. Sama’ila ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 Et il courut vers Héli, et lui dit: Me voici, car tu m'as appelé; mais [Héli] dit: Je ne t'ai point appelé, retourne[-t'en], [et] te couche; et il s'en retourna, et se coucha.
Sai ya ruga wajen Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Eli ya ce, “Ɗana ban kira ba, je ka kwanta”. Saboda haka ya tafi ya kwanta.
6 Et l'Eternel appela encore Samuel; et Samuel se leva, et s'en alla vers Héli, et lui dit: Me voici, car tu m'as appelé. Et [Héli] dit: Mon fils, je ne t'ai point appelé, retourne[-t'en], [et] te couche.
Ubangiji ya sāke kiransa ya ce, “Sama’ila!” Sama’ila ya tashi kuma ya je wurin Eli ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.”
7 Or Samuel ne connaissait point encore l'Eternel, et la parole de l'Eternel ne lui avait point encore été révélée.
Sama’ila dai bai riga ya san Ubangiji ba tukuna. Ba a kuma taɓa bayyana maganar Ubangiji a gare shi ba tukuna ba.
8 Et l'Eternel appela encore Samuel pour la troisième fois; et [Samuel] se leva, et s'en alla vers Héli, et dit: Me voici, car tu m'as appelé; [et] Héli reconnut que l'Eternel appelait ce jeune garçon.
Ubangiji ya kira Sama’ila sau na uku, Sama’ila kuma ya tashi ya tafi wurin Eli, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sai Eli ya gane cewa Ubangiji ne ke kira yaron.
9 Alors Héli dit à Samuel: Va-t'en, et te couche; et si on t'appelle, tu diras: Eternel parle, car ton serviteur écoute. Samuel donc s'en alla, et se coucha en son lieu.
Saboda haka, Eli ya gaya wa Sama’ila cewa, “Je ka kwanta, in kuma ya kira ka, ka ce masa, ‘Ya Ubangiji ka yi magana gama bawanka yana saurara.’” Sama’ila ya koma ya kwanta a wurin kwanciyarsa.
10 L'Eternel donc vint, et se tint là; et appela comme les autres fois: Samuel, Samuel; et Samuel dit: Parle, car ton serviteur écoute.
Ubangiji kuma ya zo ya tsaya a wurin, yana kira ya ce, “Sama’ila, Sama’ila!” Kamar yadda ya kira a lokutan baya. Sai Sama’ila ya ce, “Yi magana gama bawanka yana saurara.”
11 Alors l'Eternel dit à Samuel: Voici, je m'en vais faire une chose en Israël, laquelle quiconque entendra, ses deux oreilles lui corneront.
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Duba ina dab da yin wani abu a Isra’ila da zai sa kunne kowa da yake ji, yă ji tsoro.
12 En ce jour-là j'effectuerai contre Héli tout ce que j ai dit touchant sa maison; en commençant, et en achevant.
A ranar zan cika dukan maganar da na yi game da Eli da iyalinsa, daga farko har ƙarshe.
13 Car je l'ai averti que je m'en allais punir sa maison pour jamais, à cause de l'iniquité laquelle il a bien connue, qui est que ses fils se sont rendus infâmes, et il ne les a point réprimés.
Gama na gaya masa zan hukunta gidansa har abada saboda zunubin da yake sane da shi;’ya’yansa sun wulaƙantar da kansu, shi kuma bai tsawata musu ba.
14 C'est pourquoi j'ai juré contre la maison d'Héli; si jamais il se fait propitiation pour l'iniquité de la maison d'Héli, par sacrifice ou par oblation.
Saboda haka na rantse a kan gidan Eli, ‘Ba za a taɓa shafe laifin gidan Eli da hadaya ko baiko ba.’”
15 Et Samuel demeura couché jusqu'au matin, puis il ouvrit les portes de la maison de l'Eternel. Or Samuel craignait de déclarer cette vision à Héli.
Sama’ila kuwa ya kwanta har safe, sa’an nan ya buɗe ƙofofin gidan Ubangiji. Ya ji tsoro yă gaya wa Eli wahayin,
16 Mais Héli appela Samuel, et lui dit: Samuel mon fils, et il répondit: Me voici.
amma Eli ya kira shi ya ce, “Sama’ila, ɗana.” Sama’ila ya ce, “Ga ni.”
17 Et [Héli] dit: Quelle est la parole qui t'a été dite? Je te prie ne me la cache point. Ainsi Dieu te fasse, et ainsi il y ajoute, si tu me caches un seul mot de tout ce qui t'a été dit.
Eli ya ce, mene ne ya ce maka? Kada ka ɓoye mini. Allah ya yi da kai har ma fiye in ka ɓoye mini kome da ya ce maka.
18 Samuel donc lui déclara tout ce qui lui avait été dit, et ne lui en cacha rien. Et [Héli] répondit: C'est l'Eternel; qu'il fasse ce qui lui semblera bon.
Don haka sai Sama’ila ya gaya masa kome bai ɓoye masa kome ba. Sa’an nan Eli ya ce, “Shi ne Ubangiji bari yă yi abin da ya yi kyau a gare shi.”
19 Or Samuel devenait grand, et l'Eternel était avec lui, qui ne laissa point tomber à terre une seule de ses paroles.
Ubangiji kuwa yana tare da Sama’ila har girmansa bai kuma bar ko ɗaya daga maganarsa ta kāsa cika ba.
20 Et tout Israël, depuis Dan jusqu'à Béersebah, connut que c'était une chose assurée que Samuel serait Prophète de l'Eternel.
Dukan Isra’ila daga Dan har Beyersheba suka shaida amincin Sama’ila annabi ne na Ubangiji.
21 Et l'Eternel continua de se manifester dans Silo; car l'Eternel se manifestait à Samuel dans Silo par la parole de l'Eternel.
Ubangiji kuwa ya dinga bayyana a Shilo, a nan ya bayyana kansa ga Sama’ila ta wurin maganarsa.