< 1 Samuel 28 >

1 Or il arriva qu'en ces jours-là les Philistins assemblèrent leurs armées pour faire la guerre contre Israël; et Akis dit à David: Sache certainement que vous viendrez avec moi au camp, toi et tes gens.
Filistiyawa suka tattara sojojinsu domin su yaƙi Isra’ila. Akish ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.”
2 Et David répondit à Akis: Certainement tu connaîtras ce que ton serviteur fera. Et Akis dit à David: C'est pour cela que je te confierai toujours la garde de ma personne.
Dawuda ya ce, “Kai da kanka za ka ga abin da bawanka zai yi.” Akish ya ce, “Da kyau, zan sa ka zama mai kāre ni.”
3 Or Samuel était mort, et tout Israël en avait fait le deuil, et on l'avait enseveli à Rama, qui était sa ville; et Saül avait ôté du pays ceux qui avaient l'esprit de Python, et les devins.
Sama’ila dai ya riga ya rasu, dukan Isra’ila suka yi makokinsa suka binne shi a garinsa a Rama. Shawulu kuma ya kori duk masu duba da masu maitanci daga ƙasar.
4 Les Philistins donc assemblés s'en vinrent, et se campèrent à Sunem, Saül aussi assembla tout Israël, et ils se campèrent à Guilboah.
Filistiyawa suka tattaru suka yi sansani a Shunem. Shawulu ya tattara dukan Isra’ila suka yi sansani a Gilbowa.
5 Et Saül voyant le camp des Philistins eut peur, et son cœur fut fort effrayé.
Da Shawulu ya ga sojojin Filistiyawa sai ya ji tsoro, ya firgita ƙwarai.
6 Et Saül consulta l'Eternel; mais l'Eternel ne lui répondit rien, ni par des songes, ni par l'Urim, ni par les Prophètes.
Ya nemi nufin Ubangiji amma bai sami amsa daga wurin Ubangiji ko ta wurin mafarki, ko ta wurin Urim, ko ta wurin annabawa ba.
7 Et Saül dit à ses serviteurs: Cherchez-moi une femme qui ait un esprit de Python, et j'irai vers elle, et je m'enquerrai par son moyen [de ce que je dois faire]. Ses serviteurs lui dirent: Voilà, il y a une femme à Hendor qui a un esprit de Python.
Shawulu ya ce wa fadawansa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Suka ce, “Akwai guda a En Dor.”
8 Alors Saül se déguisa, et prit d'autres habits, et s'en alla, lui et deux hommes avec lui, et ils arrivèrent de nuit chez cette femme; et Saül lui dit: Je te prie, devine-moi par l'esprit de Python, et fais monter vers moi celui que je te dirai.
Sai Shawulu ya sa waɗansu tufafi ya ɓad da kama, shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare, ya ce mata, “Ki yi mini duba ta hanyar sihiri, ki hawar mini duk wanda zan faɗa miki.”
9 Mais la femme lui répondit: Voici, tu sais ce que Saül a fait, [et] comment il a exterminé du pays ceux qui ont l'esprit de Python, et les devins; pourquoi donc dresses-tu un piège à mon âme pour me faire mourir?
Amma matar ta ce masa, “Tabbatacce ka dai san abin da Shawulu ya yi, ya karkashe masu duba da masu maitanci a ƙasar. Me ya sa kake sa mini tarko, don ka sa a kashe ni?”
10 Et Saül lui jura par l'Eternel, et lui dit: L'Eternel est vivant, s'il t'arrive aucun mal pour ceci.
Shawulu ya rantse mata da Ubangiji. Ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, ba za a hukunta ki a kan wannan ba.”
11 Alors la femme dit: Qui veux-tu que je te fasse monter? Et il répondit: Fais-moi monter Samuel.
Sai matar ta ce, “Wa kake so in hauro maka?” Sai ya ce, “Ki hauro mini da Sama’ila.”
12 Et la femme voyant Samuel s'écria à haute voix, en disant à Saül: Pourquoi m'as-tu déçue? car tu es Saül.
Da matar ta ga Sama’ila sai ta yi ihu da ƙarfi ta ce wa Shawulu, “Me ya sa ka ruɗe ni? Kai ne Shawulu!”
13 Et le Roi lui répondit: Ne crains point; mais qu'as-tu vu? Et la femme dit à Saül: J'ai vu un Dieu qui montait de la terre.
Sai sarki ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Me kika gani?” Matar ta ce, “Na ga wani kurwa tana fitowa daga ƙasa.”
14 Il lui dit encore: Comment est-il fait? Elle répondit: C'est un vieillard qui monte, et il est couvert d'un manteau. Et Saül connut que c'était Samuel, et s'étant baissé le visage contre terre, il se prosterna.
Ya ce, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho sanye da taguwa ne yake haurawa.” Shawulu ya gane cewa Sama’ila ne, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
15 Et Samuel dit à Saül: Pourquoi m'as-tu troublé en me faisant monter? Et Saül répondit: Je suis dans une grande angoisse; car les Philistins me font la guerre, et Dieu s'est retiré de moi, et ne m'a plus répondu, ni par les Prophètes, ni par des songes; c'est pourquoi je t'ai appelé, afin que tu me fasses entendre ce que j'aurai à faire.
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
16 Et Samuel dit: Pourquoi donc me consultes-tu, puisque l'Eternel s'est retiré de toi, et qu'il est devenu ton ennemi?
Sama’ila ya ce, “Don me kake tambayata bayan Ubangiji ya rabu da kai? Ya zama maƙiyinka?
17 Or l'Eternel a fait selon qu'il en avait parlé par moi; car l'Eternel a déchiré le Royaume d'entre tes mains, et l'a donné à ton domestique, à David.
Ubangiji ya cika abin da ya yi magana ta wurina. Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda.
18 Parce que tu n'as point obéi à la voix de l'Eternel, et que tu n'as point exécuté l'ardeur de sa colère contre Hamalec, à cause de cela l'Eternel t'a fait ceci aujourd'hui.
Gama ba ka yi biyayya ga Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba. Saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau.
19 Et même l'Eternel livrera Israël avec toi entre les mains des Philistins, et vous serez demain avec moi, toi et tes fils; l'Eternel livrera aussi le camp d'Israël entre les mains des Philistins.
Ubangiji zai ba da Isra’ila da kuma kai ga Filistiyawa, gobe kuwa da kai da’ya’yanka za ku kasance tare da ni. Ubangiji kuma zai ba da sojojin Isra’ila a hannun Filistiyawa.”
20 Et Saül tomba aussitôt à terre tout étendu, car il fut fort effrayé des paroles de Samuel, et même les forces lui manquèrent, parce qu'il n'avait rien mangé de tout ce jour-là, ni de toute la nuit.
Da jin maganar Sama’ila sai Shawulu ya faɗi ƙasa warwas. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome ba dukan yini da kuma dukan dare.
21 Alors cette femme-là vint à Saül, et voyant qu'il avait été fort troublé, elle lui dit: Voici, ta servante a obéi à ta voix, et j'ai exposé ma vie, et j'ai obéi aux paroles que tu m'as dites;
Da matar ta zo wurin Shawulu, ta ga shi a firgice, sai ta ce masa, “Duba baranyarka ta yi maka biyayya ta yi kasai da ranta, ta yi abin da ka ce ta yi.
22 Maintenant, je te prie, que tu écoutes aussi ce que ta servante te dira: [Souffre] que je mette devant toi une bouchée de pain, afin que tu manges, et que tu aies des forces pour t'en retourner par ton chemin.
To, kai ma ka kasa kunne ga baranyarka, zan ba ka abinci ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.”
23 Et il le refusa, et dit: Je ne mangerai point. Mais ses serviteurs et la femme aussi le pressèrent tant, qu'il acquiesça à leurs paroles, et s'étant levé de terre, il s'assit sur un lit.
Sai ya ƙi. Ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da bayinsa da matar suka roƙe shi, sa’an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado.
24 Or cette femme-là avait un veau qu'elle engraissait en sa maison; et elle se hâta de le tuer, puis elle prit de la farine, et la pétrit, et en cuisit des pains sans levain.
Matar kuwa tana da maraƙin da take kiwo a gida, sai ta ɗauke shi nan da nan ta yanka. Ta ɗauki garin fulawa ta kwaɓa, ta yi waina marar yisti.
25 Ce qu'elle mit devant Saül; et devant ses serviteurs; et ils mangèrent; puis s'étant levés, ils s'en allèrent cette nuit-là.
Sai ta kawo wa Shawulu da bayinsa suka kuwa ci. A daren nan suka tashi suka tafi.

< 1 Samuel 28 >