< 1 Samuel 26 >

1 Les Ziphiens, vinrent encore vers Saül à Guibha, en disant: David ne se tient-il pas caché au coteau de Hakila, qui est vis-a-vis de Jésimon?
Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
2 Et Saül se leva, et descendit au désert de Ziph, ayant avec lui trois mille hommes d'élite d'Israël, pour chercher David au désert de Ziph.
Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
3 Et Saül se campa au coteau de Hakila, qui est vis-à-vis de Jésimon, près du chemin. Or David se tenait au désert, et il aperçut venir Saül au désert pour le poursuivre.
Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
4 Et il envoya des espions par lesquels il sut très-certainement que [Saül] était venu.
sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
5 Alors David se leva, et vint au lieu où Saul s'était campé; et David vit le lieu où Saül était couché, et Abner aussi, fils de Ner, chef de son armée; or Saül était couché dans le rond [du camp], et le peuple était campé autour de lui.
Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
6 Et David s'en entretint et en parla à Ahimélec, Héthien, et à Abisaï fils de Tseruja, [et] frère de Joab, en disant: Qui descendra avec moi vers Saül au camp? Et Abisaï répondit: J'y descendrai avec toi.
Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
7 David donc et Abisaï vinrent de nuit vers le peuple, et voici, Saül dormait étant couché dans le rond [du camp], et sa hallebarde était fichée en terre à son chevet; et Abner, et le peuple étaient couchés autour de lui.
Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
8 Alors Abisaï dit à David: Aujourd'hui Dieu a livré ton ennemi entre tes mains; maintenant donc que je le frappe, je te prie, de la hallebarde, jusqu'en terre d'un seul coup, et je n'y retournerai pas une seconde fois.
Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
9 Et David dit à Abisaï: Ne le mets point à mort; car qui est-ce qui mettra sa main sur l'Oint de l'Eternel, et sera innocent?
Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
10 David dit encore: L'Eternel est vivant, si ce n'est que l'Eternel le frappe, ou que son jour vienne, ou qu'il descende dans une bataille, et qu'il y demeure;
Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
11 Que l'Eternel me garde de mettre ma main sur l'Oint de l'Eternel; mais je te prie, prends maintenant la hallebarde qui est à son chevet, et le pot à eau, et allons-nous-en.
Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
12 David donc prit la hallebarde et le pot à eau qui étaient au chevet de Saül, puis ils s'en allèrent; et il n'y eut personne qui les vît, ni qui les aperçût, ni qui s'éveillât; car ils dormaient tous; à cause que l'Eternel avait fait tomber sur eux un profond sommeil.
Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
13 Et David passa de l'autre côté, et s'arrêta sur le haut de la montagne, loin de là; car il y avait une grande distance entr'eux.
Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
14 Et il cria au peuple, et à Abner fils de Ner, en disant: Ne répondras-tu pas, Abner? Et Abner répondit, et dit: Qui es-tu qui cries au Roi?
Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
15 Alors David dit à Abner: N'es-tu pas un vaillant homme? et qui est semblable à toi en Israël? pourquoi donc n'as-tu pas gardé le Roi ton Seigneur? car quelqu'un du peuple est venu pour tuer le Roi ton Seigneur.
Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
16 Ce n'est pas bien fait à toi; l'Eternel est vivant, que vous êtes dignes de mort, pour avoir si mal gardé votre Seigneur, l'Oint de l'Eternel; et maintenant regarde où est la hallebarde du Roi, et le pot à eau qui était à son chevet.
Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
17 Alors Saül reconnut la voix de David, et dit: N'est-ce pas là ta voix, mon fils David? Et David dit: C'est ma voix, ô Roi mon Seigneur.
Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
18 Il dit encore: Pourquoi mon Seigneur poursuit-il son serviteur? car qu'ai-je fait, et quel mal y a-t-il en ma main?
Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
19 Maintenant donc je te prie, que le Roi mon Seigneur écoute les paroles de son serviteur. Si c'est l'Eternel qui te pousse contre moi, que ton oblation lui soit agréable; mais si ce sont les hommes, ils sont maudits devant l'Eternel; car aujourd'hui ils m'ont chassé, afin que je ne me tienne point joint à l'héritage de l'Eternel, [et ils m'ont] dit: Va, sers les dieux étrangers.
To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
20 Et maintenant, que mon sang ne tombe point en terre devant l'Eternel; car le Roi d'Israël est sorti pour chercher une puce, [et] comme qui poursuivrait une perdrix dans les montagnes.
Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
21 Alors Saül dit: J'ai péché, retourne-t'en, mon fils David; car je ne te ferai plus de mal, parce qu'aujourd'hui ma vie t'a été précieuse. Voici, j'ai agi follement, et j'ai fait une très-grande faute.
Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
22 Et David répondit, et dit: Voici la hallebarde du Roi; que quelqu'un des vôtres passe ici, et la prenne.
Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
23 Or que l'Eternel rende à chacun selon sa justice, et [selon] sa fidélité; car il t'avait livré aujourd'hui entre mes mains, mais je n'ai point voulu mettre ma main sur l'Oint de l'Eternel.
Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
24 Voici donc, comme ton âme a été aujourd'hui de grand prix devant mes yeux, ainsi mon âme sera de grand prix devant les yeux de l'Eternel, et il me délivrera de toutes les afflictions.
Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
25 Et Saül dit à David: Béni sois-tu, mon fils David; tu ne manqueras pas de réussir, et d'avoir le dessus. Alors David continua son chemin, et Saül s'en retourna en son lieu.
Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.

< 1 Samuel 26 >