< 1 Samuel 22 >

1 Or David partit de là, et se sauva dans la caverne d'Hadullam; ce que ses frères et toute la maison de son père ayant appris, ils descendirent là vers lui.
Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
2 Tous ceux aussi qui étaient mal dans leurs affaires, et qui avaient des créanciers [dont ils étaient tourmentés], et qui avaient le cœur plein d'amertume, s'assemblèrent vers lui, et il fut leur chef; et il y eut avec lui environ quatre cents hommes.
Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
3 Et David s'en alla de là à Mitspé de Moab; et il dit au Roi de Moab: Je te prie que mon père et ma mère se retirent vers vous jusqu'à ce que je sache ce que Dieu fera de moi.
Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
4 Et il les amena devant le Roi de Moab, et ils demeurèrent avec lui, tout le temps que David fut dans cette forteresse.
Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
5 Or Gad le prophète dit à David: Ne demeure point dans cette forteresse, [mais] va-t'en, et entre dans le pays de Juda. David donc s'en alla, et vint en la forêt de Hérets.
Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
6 Et Saül apprit qu'on avait découvert David et les gens qui étaient avec lui. Or Saül était assis au coteau sous un chêne à Rama, ayant sa hallebarde en sa main, et tous ses serviteurs se tenaient devant lui.
Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
7 Et Saül dit à ses serviteurs qui se tenaient devant lui: Ecoutez maintenant, Benjamites: Le fils d'Isaï vous donnera-t-il à vous tous des champs et des vignes? Vous établira-t-il tous gouverneurs sur milliers, et sur centaines?
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
8 Que vous ayez tous conspiré contre moi, et qu'il n'y ait personne qui m'avertisse que mon fils a fait alliance avec le fils d'Isaï, et qu'il n'y ait aucun de vous qui ait pitié de moi, et qui m'avertisse; car mon fils a suscité mon serviteur contre moi pour me dresser des embûches, comme il paraît aujourd'hui.
Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
9 Alors Doëg Iduméen, qui était établi sur les serviteurs de Saül, répondit, et dit: J'ai vu le fils d'Isaï venir à Nob vers Ahimélec fils d'Ahitub;
Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
10 Qui a consulté l'Eternel pour lui, et lui a donné des vivres, et l'épée de Goliath le Philistin.
Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
11 Alors le Roi envoya appeler Ahimélec le Sacrificateur fils d'Ahitub, et toute la famille de son père, [savoir] les Sacrificateurs qui étaient à Nob; et ils vinrent tous vers le Roi.
Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
12 Et Saül dit: Ecoute maintenant, fils d'Ahitub; et il répondit: Me voici, mon Seigneur.
Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
13 Alors Saül lui dit: Pourquoi avez-vous conspiré contre moi, toi et le fils d'Isaï, vu que tu lui as donné du pain, et une épée, et que tu as consulté Dieu pour lui, afin qu'il s'élevât contre moi pour me dresser des embûches, comme il paraît aujourd'hui.
Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
14 Et Ahimélec répondit au Roi, et dit: Entre tous tes serviteurs y en a-t-il un comme David, qui est fidèle, et gendre du Roi, et qui est parti par ton commandement, et qui est si honoré en ta maison?
Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
15 Ai-je commencé aujourd'hui à consulter Dieu pour lui? A Dieu ne plaise! Que le Roi ne charge donc d'aucune chose son serviteur, ni toute la maison de mon père; car ton serviteur ne sait chose ni petite ni grande de tout ceci.
A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
16 Et le Roi lui dit: Certainement tu mourras, Ahimélec, et toute la famille de ton père.
Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
17 Alors le Roi dit aux archers qui se tenaient devant lui: Tournez-vous, et faites mourir les Sacrificateurs de l'Eternel; car ils sont aussi de la faction de David parce qu'ils ont bien su qu'il s'enfuyait, et qu'ils ne m'en ont point averti. Mais les serviteurs du Roi ne voulurent point étendre leurs mains, pour se jeter sur les Sacrificateurs de l'Eternel.
Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
18 Alors le Roi dit à Doëg: Tourne-toi, et te jette sur les Sacrificateurs; et Doëg Iduméen se tourna, et se jeta sur les Sacrificateurs; et il tua en ce jour-là quatre vingt cinq hommes qui portaient l'Ephod de lin.
Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
19 Et il fit passer Nob, ville des Sacrificateurs, au fil de l'épée, les hommes et les femmes, les grands et ceux qui tètent, même [il fit passer] les bœufs, les ânes, et le menu bétail au fil de l'épée.
Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
20 Toutefois un des fils d'Ahimélec, fils d'Ahitub, qui avait nom Abiathar, se sauva, et s'enfuit auprès de David.
Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
21 Et Abiathar rapporta à David, que Saül avait tué les Sacrificateurs de l'Eternel.
Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
22 Et David dit à Abiathar: Je connus bien en ce jour-là, puisque Doëg Iduméen était là, qu'il ne manquerait pas de le rapporter à Saül; je suis cause [de ce qui est arrivé] à toutes les personnes de la famille de ton père.
Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
23 Demeure avec moi, ne crains point; car celui qui cherche ma vie, cherche la tienne; certainement tu seras gardé avec moi.
Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”

< 1 Samuel 22 >