< 1 Samuel 2 >
1 Alors Anne pria, et dit: Mon cœur s'est réjoui en l'Eternel; ma corne a été élevée par l'Eternel; ma bouche s'est ouverte sur mes ennemis, parce que je me suis réjouie de ton salut.
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
2 Il n'y a nul saint comme l'Eternel; car il n'y en a point d'autre que toi, et il n'y a point de Rocher tel que notre Dieu.
“Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3 Ne proférez point tant de paroles hautaines, hautaines; qu'il ne sorte point de votre bouche des paroles rudes; car l'Eternel est le [Dieu] Fort des sciences; c'est à lui à peser les entreprises.
“Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
4 L'arc des forts a été brisé; mais ceux qui ne faisaient que chanceler, ont été ceints de force.
“An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
5 Ceux qui avaient accoutumé d'être rassasiés, se sont loués pour du pain; mais les affamés ont cessé [de l'être], et même la stérile en a enfanté sept; et celle qui avait beaucoup de fils est devenue languissante.
Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
6 L'Eternel est celui qui fait mourir, et qui fait vivre; qui fait descendre au sépulcre, et qui [en] fait remonter. (Sheol )
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol )
7 L'Eternel appauvrit, et enrichit; il abaisse et il élève.
Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
8 Il élève le pauvre de la poudre, et il tire le misérable de dessus le fumier, pour le faire asseoir avec les principaux, et il leur donne en héritage un trône de gloire; car les fondements de la terre sont à l'Eternel, et il a posé sur eux la terre habitable.
Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
9 Il gardera les pieds de ses bien-aimés, et les méchants se tairont dans les ténèbres; car l'homme ne sera point le plus fort par sa force.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
10 Ceux qui contestent contre l'Eternel seront froissés; il tonnera des cieux sur chacun d'eux; l'Eternel jugera les bouts de la terre; et il donnera la force à son Roi, et élèvera la corne de son oint.
waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
11 Puis Elkana s'en alla à Rama en sa maison, et le jeune garçon vaquait au service de l'Eternel, en la présence d'Héli le Sacrificateur.
Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
12 Or les fils d'Héli étaient de méchants hommes; ils ne connaissaient point l'Eternel,
’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
13 Car le train ordinaire de ces Sacrificateurs-là envers le peuple, [était, que] quand quelqu'un faisait quelque sacrifice, le garçon du Sacrificateur venait lorsqu'on faisait bouillir la chair, ayant en sa main une fourchette à trois dents,
Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
14 Avec laquelle il frappait dans la chaudière, ou dans le chauderon, ou dans la marmite, ou dans le pot; [et] le Sacrificateur prenait pour soi tout ce que la fourchette enlevait; ils en faisaient ainsi à tous ceux d'Israël qui venaient là à Silo.
zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
15 Même avant qu'on fît fumer la graisse, le garçon du Sacrificateur venait, et disait à l'homme qui sacrifiait: Donne-moi de la chair à rôtir pour le Sacrificateur; car il ne prendra point de toi de chair bouillie, mais de la chair crue.
Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
16 Que si l'homme lui répondait: Qu'on ne manque pas de faire fumer tout présentement la graisse; et après cela prends ce que ton âme souhaitera; alors il lui disait: Quoi qu'il en soit, tu en donneras maintenant; et si tu ne m'en donnes, j'en prendrai par force.
In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
17 Et le péché de ces jeunes hommes fut très-grand devant l'Eternel; car les gens en méprisaient l'oblation de l'Eternel.
Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
18 Or Samuel servait en la présence de l'Eternel, étant jeune garçon, vêtu d'un Ephod de lin.
Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
19 Sa mère lui faisait un petit roquet, qu'elle lui apportait tous les ans, quand elle montait avec son mari pour offrir le sacrifice solennel.
Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
20 Et Héli bénit Elkana et sa femme, et dit: L'Eternel te fasse avoir des enfants de cette femme, pour le prêt qui a été fait à l'Eternel. Et ils s'en retournèrent chez eux.
Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
21 Et l'Eternel visita Anne, laquelle conçut et enfanta trois fils et deux filles; et le jeune garçon Samuel devint grand en la présence de l'Eternel.
Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
22 Or Héli était fort vieux, et il apprit tout ce que faisaient ses fils à tout Israël, et qu'ils couchaient avec les femmes qui s'assemblaient par troupes à la porte du Tabernacle d'assignation.
To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
23 Et il leur dit: Pourquoi faites-vous ces actions-là? car j'apprends vos méchantes actions; ces choses [me viennent] de tout le peuple.
Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
24 Ne faites pas ainsi, mes fils; car ce que j'entends dire de vous n'est pas bon; vous faites pécher le peuple de l'Eternel.
A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
25 Si un homme a péché contre un autre homme, le Juge en jugera; mais si quelqu'un pèche contre l'Eternel, qui est-ce qui priera pour lui? Mais ils n'obéirent point à la voix de leur père, parce que l'Eternel voulait les faire mourir.
In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
26 Cependant le jeune garçon Samuel croissait et il était agréable à l'Eternel et aux hommes.
Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
27 Or un homme de Dieu vint à Héli, et lui dit: Ainsi a dit l'Eternel: Ne me suis-je pas clairement manifesté à la maison de ton père, quand ils étaient en Egypte, en la maison de Pharaon?
Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
28 Je l'ai aussi choisi d'entre toutes les Tribus d'Israël pour être mon Sacrificateur, afin d'offrir sur mon autel, [et] faire fumer les parfums, [et] porter l'Ephod devant moi; et j'ai donné à la maison de ton père toutes les oblations des enfants d'Israël faites par le feu.
Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
29 Pourquoi avez-vous regimbé contre mon sacrifice, et contre mon oblation que j'ai commandé de faire dans le Tabernacle? et [pourquoi] as-tu honoré tes fils plus que moi, pour vous engraisser du meilleur de toutes les offrandes d'Israël mon peuple?
Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
30 C'est pourquoi l'Eternel le Dieu d'Israël dit: J'avais dit certainement que ta maison et la maison de ton père marcheraient devant moi éternellement; mais maintenant l'Eternel dit: Il ne sera pas dit que je fasse cela; car j'honorerai ceux qui m'honorent, mais ceux qui me méprisent seront traités avec le dernier mépris.
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
31 Voici les jours viennent que je couperai ton bras, et le bras de la maison de ton père, tellement qu'il n'y aura aucun homme en ta maison qui devienne vieux.
Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
32 Et tu verras un adversaire [établi dans] le Tabernacle, au temps que [Dieu] enverra toute sorte de biens à Israël; et il n'y aura jamais en ta maison aucun homme qui devienne vieux.
Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
33 Et celui [de tes descendants que] je n'aurai point retranché d'auprès de mon autel, sera pour faire défaillir tes yeux, et affliger ton âme; et tous les enfants de ta maison mourront en la fleur de l'âge.
Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
34 Et ceci t'en sera le signe, [savoir] ce qui arrivera à tes deux fils, Hophni et Phinées, c'est qu'ils mourront tous deux en un même jour.
“‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
35 Et je m'établirai un Sacrificateur assuré; il fera selon ce qui est en mon cœur, et selon mon âme; et je lui édifierai une maison assurée, et il marchera à toujours devant mon Oint.
Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
36 Et il arrivera que quiconque sera resté de ta maison, viendra se prosterner devant lui pour avoir une pièce d'argent, [et] quelque pain, et dira: Donne-moi une place, je te prie, dans quelqu'une des charges de la Sacrificature, pour manger un morceau de pain.
Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”