< 1 Rois 5 >

1 Hiram aussi Roi de Tyr envoya ses serviteurs vers Salomon, ayant appris qu'on l'avait oint pour Roi en la place de son père; car Hiram avait toujours aimé David.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Et Salomon envoya vers Hiram pour lui dire:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 Tu sais que David mon père n'a pu bâtir une maison au Nom de l'Eternel son Dieu, à cause des guerres qui l'ont environné, jusqu'à ce que l'Eternel a eu mis ses [ennemis] sous ses pieds.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 Et maintenant l'Eternel mon Dieu m'a donné du repos tout alentour, et je n'ai point d'ennemis, ni d'affaire fâcheuse.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Voici donc je prétends bâtir une maison au Nom de l'Eternel mon Dieu, selon que l'Eternel en a parlé à David mon père en disant: Ton fils que je mettrai en ta place sur ton trône sera celui qui bâtira une maison à mon Nom.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 C'est pourquoi commande maintenant qu'on coupe des cèdres du Liban, et que mes serviteurs soient avec tes serviteurs; et je te donnerai pour tes serviteurs telle récompense que tu me diras; car tu sais qu'il n'y a point de gens parmi nous qui s'entendent comme les Sidoniens, à couper le bois.
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 Or il arriva que quand Hiram eut entendu les paroles de Salomon, il s'en réjouit fort, et dit: Béni soit aujourd'hui l'Eternel, qui a donné à David un fils sage [pour être Roi] sur ce grand peuple.
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 Hiram envoya donc vers Salomon pour [lui] dire: J'ai entendu ce que tu m'as envoyé dire, et je ferai tout ce que tu veux au sujet du bois de cèdre et du bois de sapin.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 Mes serviteurs les amèneront depuis le Liban jusqu'à la mer, puis je les ferai mettre sur la mer par radeaux, jusqu'au lieu que tu m'auras marqué, et je les ferai là délier, et tu les prendras, et de ton côté tu me satisferas en fournissant de vivres ma maison.
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 Hiram donc donnait du bois de cèdre et du bois de sapin à Salomon, autant qu'il en voulait.
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 Et Salomon donnait à Hiram vingt mille Cores de froment pour la nourriture de sa maison, et vingt Cores d'huile très-pure; Salomon en donnait autant à Hiram chaque année.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 Et l'Eternel donna de la sagesse à Salomon, comme l'Eternel lui [en] avait parlé; et il y eut paix entre Hiram et Salomon, et ils traitèrent alliance ensemble.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 Le Roi Salomon fit aussi une levée [de gens] sur tout Israël, et la levée fut de trente mille hommes.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 Et il en envoyait dix mille au Liban chaque mois, tour à tour, ils étaient un mois au Liban, et deux mois en leur maison; et Adoniram [était commis] sur cette levée.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 Salomon avait aussi soixante-dix mille hommes qui portaient les faix, et quatre-vingt mille qui coupaient le bois sur la montagne;
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 Sans les Chefs des Commis de Salomon, qui avaient la charge de l'ouvrage, au nombre de trois mille trois cents, lesquels commandaient au peuple qui était employé à ce travail.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 Et par le commandement du Roi, on amena de grandes pierres, et des pierres de prix, pour faire le fondement de la maison, qui étaient toutes taillées.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 De sorte que les maçons de Salomon, et les maçons d'Hiram, et les tailleurs de pierres taillèrent et préparèrent le bois et les pierres pour bâtir la maison.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.

< 1 Rois 5 >