< 1 Rois 2 >

1 Or le temps de la mort de David étant proche, il donna ce commandement à son fils Salomon, disant:
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 Je m'en vais par le chemin de toute la terre, fortifie-toi, et porte-toi en homme.
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 Et garde ce que l'Eternel ton Dieu veut que tu gardes, en marchant dans ses voies, et en gardant ses statuts, ses commandements, ses ordonnances, et ses témoignages, selon ce qui est écrit dans la Loi de Moïse, afin que tu réussisses en tout ce que tu feras, et en tout ce que tu entreprendras;
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 Afin que l'Eternel confirme la parole qu'il m'a donnée, en disant: Si tes fils prennent garde à leur voie, pour marcher devant moi dans la vérité, de tout leur cœur, et de toute leur âme, il ne te manquera point [de successeur] assis sur le trône d'Israël.
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 Au reste, tu sais ce que m'a fait Joab fils de Tséruja, et ce qu'il a fait aux deux Chefs des armées d'Israël, Abner fils de Ner, et Hamasa fils de Jéther, qu'il a tués, ayant répandu durant la paix le sang qu'on répand en temps de guerre, et ayant ensanglanté de ce sang qu'on répand en temps de guerre, la ceinture qu'il avait sur ses reins; et les souliers qu'il avait en ses pieds.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Tu en feras donc selon ta sagesse, en sorte que tu ne laisseras point descendre paisiblement ses cheveux blancs au sépulcre. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 Mais tu feras du bien aux enfants de Barzillaï Galaadite, et ils seront du nombre de ceux qui mangent à ta table, parce qu'ils se sont ainsi approchés de moi quand je m'enfuyais de devant Absalom ton frère.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Voilà de plus avec toi Simhi, fils de Guéra, fils de Jémini de Bahurim, qui proféra contre moi des malédictions atroces, le jour que je m'en allais à Mahanajim; mais il descendit au devant de moi vers le Jourdain, et je lui jurai par l'Eternel, en disant: Je ne te ferai point mourir par l'épée.
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 Maintenant donc tu ne le laisseras point impuni; car tu es sage, pour savoir ce que tu lui devras faire; et tu feras descendre ses cheveux blancs au sépulcre par une mort violente. (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 Ainsi David s'endormit avec ses pères, et fut enseveli dans la Cité de David.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 Et le temps que David régna sur Israël, fut quarante ans. Il régna sept ans à Hébron, et il régna trente-trois ans à Jérusalem.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 Et Salomon s'assit sur le trône de David son père, et son Royaume fut fort affermi.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 Alors Adonija fils de Haggith, vint vers Bath-sebah, mère de Salomon, et elle dit: Viens-tu à bonne intention? et il répondit: [Je viens] à bonne intention.
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 Puis il dit: J'ai un mot à te [dire]. Elle répondit: Parle.
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 Et il dit: Tu sais bien que le Royaume m'appartenait, et que tout Israël s'attendait que je régnerais; mais le Royaume a été transféré, et il est échu à mon frère; parce que l'Eternel le lui a donné.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Maintenant donc j'ai à te faire une prière, ne me la refuse point. Et elle lui répondit: Parle.
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 Et il dit: Je te prie, dis au Roi Salomon, car il ne te refusera rien, qu'il me donne Abisag Sunamite pour femme.
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 Et Bath-sebah répondit: Et bien, je parlerai pour toi au Roi.
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 Bath-sebah vint donc au Roi Salomon lui parler pour Adonija; et le Roi se leva [pour aller] au devant de Bath-sebah, et se prosterna devant elle; puis il s'assit sur son trône, et fit mettre un siège pour sa mère, et elle s'assit à la main droite du Roi;
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 Et dit: J'ai à te faire une petite demande, ne me la refuse point. Et le Roi lui répondit: Fais-la, ma mère; car je ne te la refuserai point.
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 Et elle dit: Qu'on donne Abisag Sunamite pour femme à Adonija ton frère.
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 Mais le Roi Salomon répondit à sa mère, et dit: et pourquoi demandes-tu Abisag Sunamite pour Adonija? demande plutôt le Royaume pour lui, parce qu'il est mon frère plus âgé que moi; [demande-le] pour lui, pour Abiathar le Sacrificateur, et pour Joab fils de Tséruja.
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Alors le Roi Salomon jura par l'Eternel, en disant: Que Dieu me fasse ainsi, et qu'ainsi il y ajoute, si Adonija n'a dit cette parole contre sa vie!
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 Or maintenant l'Eternel, qui m'a établi, et qui m'a fait asseoir sur le trône de David mon père, et qui m'a édifié une maison, comme il avait dit, est vivant, que certainement Adonija sera aujourd'hui mis à mort.
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 Et le Roi Salomon donna commission à Bénaja fils de Jéhojadah, qui se jeta sur lui, et il mourut.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 Puis le Roi dit à Abiathar Sacrificateur: Va-t'en à Hanathoth dans ta possession, car tu mérites la mort; toutefois je ne te ferai point mourir aujourd'hui, parce que tu as porté l'Arche du Seigneur l'Eternel devant David mon père; et parce que tu as eu part à toutes les afflictions de mon père.
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 Ainsi Salomon déposa Abiathar, afin qu'il ne fût plus Sacrificateur de l'Eternel; pour accomplir la parole de l'Eternel, qu'il avait prononcée en Silo contre la maison d'Héli.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 Et le bruit en étant venu jusqu'à Joab, qui s'était révolté pour suivre Adonija, quoiqu'il ne se fût point détourné après Absalom, il s'enfuit au Tabernacle de l'Eternel, et empoigna les cornes de l'autel.
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 Et on le rapporta au Roi Salomon, en disant: Joab s'en est enfui au Tabernacle de l'Eternel, et voilà, il est auprès de l'autel. Et Salomon envoya Bénaja fils de Jéhojadah, et lui dit: Va, jette-toi sur lui.
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 Bénaja donc entra au Tabernacle de l'Eternel, et dit à Joab: Ainsi a dit le Roi: Sors de là. Et il répondit: Non, mais je mourrai ici. Et Bénaja le rapporta au Roi, et dit: Joab m'a parlé ainsi, et m'a ainsi répondu.
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 Et le Roi lui dit: Fais comme il t'a dit, et jette-toi sur lui, et l'ensevelis; et tu ôteras de dessus moi, et de dessus la maison de mon père, le sang que Joab a répandu sans cause.
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 Et l'Eternel fera retomber son sang sur sa tête, car il s'est jeté sur deux hommes plus justes et meilleurs que lui, et les a tués avec l'épée, sans que David mon père en sût rien; [savoir] Abner fils de Ner, chef de l'armée d'Israël; et Hamasa fils de Jéther, chef de l'armée de Juda.
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 Et leur sang retombera sur la tête de Joab, et sur la tête de sa postérité à toujours; mais il y aura paix de par l'Eternel, à toujours pour David, et pour sa postérité, et pour sa maison, et pour son trône.
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 Bénaja donc fils de Jéhojadah monta, et se jeta sur lui, et le tua; et on l'ensevelit dans sa maison au désert.
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 Alors le Roi établit Bénaja fils de Jéhojadah sur l'armée en la place de Joab; le Roi établit aussi Tsadok Sacrificateur en la place d'Abiathar.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Puis le Roi envoya appeler Simhi, et lui dit: Bâtis-toi une maison à Jérusalem, et y demeure, et n'en sors point [pour aller] de côté ou d'autre.
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 Car sache que le jour que tu en sortiras, et que tu passeras le torrent de Cédron, tu mourras certainement; ton sang sera sur ta tête.
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 Et Simhi répondit au Roi: Cette parole est bonne, ton serviteur fera tout ce que le Roi mon Seigneur a dit. Ainsi Simhi demeura à Jérusalem plusieurs jours.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 Mais il arriva qu'au bout de trois ans, deux serviteurs de Simhi s'enfuirent vers Akis, fils de Mahaca Roi de Gath, et on le rapporta à Simhi en disant: Voilà tes serviteurs sont à Gath.
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 Alors Simhi se leva, et sella son âne, et s'en alla à Gath vers Akis, pour chercher ses serviteurs; ainsi Simhi s'en alla, et ramena ses serviteurs de Gath.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 Et on rapporta à Salomon que Simhi était allé de Jérusalem à Gath, et qu'il était de retour.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 Et le Roi envoya appeler Simhi, et lui dit: Ne t'avais-je pas fait jurer par l'Eternel, et ne t'avais-je pas protesté, disant: Sache certainement que le jour que tu seras sorti, et que tu seras allé çà ou là, tu mourras certainement? et ne me répondis-tu pas: La parole que j'ai entendue est bonne?
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 Pourquoi donc n'as-tu pas gardé le serment que tu as fait par l'Eternel, et le commandement que je t'avais fait?
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 Le Roi dit aussi à Simhi: Tu sais tout le mal que tu as fait à David mon père, et tu en es convaincu dans ton cœur; c'est pourquoi l'Eternel a fait retomber ton mal sur ta tête.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 Mais le Roi Salomon sera béni, et le trône de David sera affermi devant l'Eternel à jamais.
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Et le Roi donna commission à Bénaja fils de Jéhojadah, qui sortit, et se jeta sur lui; et il mourut. Et le Royaume fut affermi entre les mains de Salomon.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Rois 2 >