< 1 Chroniques 9 >
1 Ainsi tous ceux d'Israël furent rangés par généalogie, et voilà, ils sont écrits au Livre des Rois d'Israël; et ceux de Juda furent transportés à Babylone à cause de leurs péchés.
Haka aka lissafta dukan Isra’ila a tarihin zuriyoyi a littafin sarakunan Isra’ila. Aka kwasa mutanen Yahuda zuwa zaman bauta a Babilon domin rashin aminci.
2 Mais ce sont ici les premiers qui habitèrent dans leurs possessions, [et] dans leurs villes, tant d'Israël, que des Sacrificateurs, des Lévites, et des Néthiniens.
To, na farkon da aka sāke zaunar da su a mallakarsu a garuruwansu, su ne waɗansu Isra’ilawa, firistoci, Lawiyawa da kuma masu hidimar haikali.
3 Et il demeura dans Jérusalem, des enfants de Juda, des enfants de Benjamin, et des enfants d'Ephraïm et de Manassé.
Waɗanda suke daga Yahuda, daga Benyamin, da kuma daga Efraim da Manasse waɗanda suka zauna a Urushalima su ne,
4 Huthaï fils d'Hammihud, fils de Homri, fils d'Imri, fils de Bani, des enfants de Pharez, fils de Juda.
Uttai ɗan Ammihud, ɗan Omri, ɗan Imri, ɗan Bani, zuriyar Ferez ɗan Yahuda.
5 Et des Silonites, Hasaïa le premier-né, et ses fils.
Na mutanen Shilo kuwa su ne, Asahiya ɗan fari da’ya’yansa maza.
6 Et des enfants de Zara, Jéhuël, et ses frères, six cent quatre-vingt et dix.
Na mutanen Zera su ne, Yewuyel. Mutane daga Yahuda sun kai 690.
7 Et des enfants de Benjamin, Sallu fils de Mésullam, fils de Hodavia, fils de Hassenua.
Na Benyamin su ne, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Hodawiya, ɗan Hassenuwa;
8 Et Jibnéja fils de Jéroham, et Ela fils de Huzi, fils de Micri; et Mésullam fils de Saphatia, fils de Réhuël, fils de Jibnija.
Ibnehiya ɗan Yeroham; Ela ɗan Uzzi, ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya, ɗan Reyuwel, ɗan Ibniya.
9 Leurs frères, selon leurs générations, furent neuf cent cinquante-six. Tous ces hommes-là furent chefs des pères, selon la maison de leurs pères.
Mutane daga Benyamin, kamar yadda aka lissafta zuriyarsu, sun kai 956. Dukan waɗannan mutane kawunan iyalansu ne.
10 Et des Sacrificateurs, Jédahja, Jéhojarib, et Jakin.
Na firistoci su ne, Yedahiya; Yehoyarib; Yakin;
11 Et Hazaria fils de Hilkija, fils de Mésullam, fils de Tsadoc, fils de Mérajoth, fils d'Ahitub, conducteur de la maison de Dieu.
Azariya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, shugaban da yake lura da gidan Allah;
12 Et Hadaja fils de Jéroham, fils de Pashur, fils de Malkija; et Mahasaï, fils d'Hadiël, fils de Jahzéra, fils de Mésullam, fils de Mésillémith, fils d'Immer.
Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya; da Ma’asai ɗan Adiyel, ɗan Yazera, ɗan Meshullam, ɗan Meshillemit, ɗan Immer.
13 Et leurs frères chefs en la maison de leurs pères, mille sept cent soixante hommes, forts et vaillants, pour faire l'œuvre du service de la maison de Dieu.
Firistocin da suke kawunan iyalai, sun kai 1,760. Dukansu ƙwararru ne, masu hakkin hidima a cikin gidan Allah.
14 Et les Lévites, Sémahja, fils de Hasub, fils de Hazrikam, fils de Hasabia, des enfants de Mérari,
Na Lawiyawa su ne, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, mutumin Merari;
15 Bakbakar, Hérès, et Galal; et Mattania fils de Mica, fils de Zicri, fils d'Asaph.
Bakbakkar, Heresh, Galal da Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zikri, ɗan Asaf;
16 Et Hobadia fils de Sémathia, fils de Galal, fils de Jéduthun; et Bérécia, fils d'Asa, fils d'Elkana, qui habita dans les bourgs des Nétophatiens.
Obadiya ɗan Shemahiya, ɗan Galal, ɗan Yedutun; da Berekiya ɗan Asa, ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofawa.
17 Et quant aux portiers, Sallum, Hakkub, Talmon, et Ahiman, et leurs frères; [mais] Sallum était le chef;
Matsaran ƙofofi su ne, Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman da’yan’uwansu. Shallum ne babbansu
18 [Et il l'a été] jusqu'à maintenant, [ayant la charge] de la porte du Roi vers l'Orient. Ceux-là furent portiers selon les familles des enfants de Lévi.
da aka ajiye a Ƙofar Sarki a gabas, har zuwa wannan lokaci. Waɗannan su ne matsaran ƙofofi na sansanin Lawiyawa.
19 Et Sallum fils de Coré, fils d'Ebiasaph, fils de Coré, et ses frères Corites, selon la maison de son père, avaient la charge de l'ouvrage du service, gardant les vaisseaux du Tabernacle, comme leurs pères en avaient gardé l'entrée au camp de l'Eternel,
Shallum ɗan Kore, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, da’yan’uwansa matsaran ƙofofi daga iyalin (mutanen Kohat) su suke da hakkin tsaron madogaran ƙofar Tenti kamar dai yadda kakanninsu suka kasance da hakkin tsaron mashigin mazaunin Ubangiji.
20 Lorsque Phinées, fils d'Eléazar, fut établi chef sur eux en la présence de l'Eternel, qui était avec lui.
A dā Finehas ɗan Eleyazar ne yake lura da matsaran, kuma Ubangiji ya kasance tare da shi.
21 Et Zacharie fils de Mésélémia [était] le portier de l'entrée du Tabernacle d'assignation.
Zakariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaro a mashigin Tentin Sujada.
22 Ce sont là tous ceux qui furent choisis pour être les portiers des entrées, deux cent et douze; qui furent mis selon les familles par généalogie, selon leurs bourgs, comme David et Samuël le Voyant les avaient établis dans leur office.
Duka-duka, waɗanda aka zaɓa don su zama matsaran madogaran ƙofa sun kai 212. Aka rubuta su zuriya-zuriya a ƙauyukansu. Dawuda da Sama’ila mai duba ne suka sa matsaran a wurarensu na aminci.
23 Eux, [dis-je], et leurs enfants furent établis sur les portes de la maison de l'Eternel, qui est la maison du Tabernacle, pour y faire la garde.
Su da zuriyarsu, su suke lura da tsaron ƙofofin gidan Ubangiji, gidan da ake kira Tenti.
24 Les portiers devaient être vers les quatre vents; [savoir], vers l'Orient et l'Occident, vers le Septentrion et le Midi.
Matsaran suna a kusurwoyi huɗu, gabas, yamma, arewa da kudu.
25 Et leurs frères, qui étaient dans leurs bourgs, devaient venir avec eux de sept jours en sept jours, de temps en temps.
’Yan’uwansu a ƙauyukansu sukan zo lokaci, lokaci su yi ayyukansu kwana bakwai, bakwai.
26 Car selon cet ordre, il y avait toujours quatre maîtres-portiers, Lévites, qui étaient même commis sur les chambres, et sur les trésors de la maison de Dieu.
Amma manyan matsara huɗu, waɗanda suke Lawiyawa, an danƙa musu hakkin lura da ɗakuna da kuma wuraren ajiya a gidan Allah.
27 Et ils se tenaient la nuit tout autour de la maison de Dieu; car la garde leur en appartenait, et ils avaient la charge de l'ouvrir tous les matins.
Sukan kwana a kewayen gidan Allah, domin dole su tsare shi; kuma su suke lura da mabuɗi don buɗewa a kowace safiya.
28 Il y en avait aussi quelques-uns d'entr'eux commis sur les vaisseaux du service; car on les portait dans le [Temple], par compte, et on les en tirait par compte.
Waɗansunsu su ne suke lura da kayayyakin da ake amfani da su a hidimar haikali; sukan ƙirga su sa’ad da ake shigar da su da sa’ad da ake fitar da su.
29 Il y en avait aussi qui étaient commis sur les autres ustensiles, et sur tous les vaisseaux consacrés, et sur la fleur de farine, et sur le vin, et sur l'huile, et sur l'encens, et sur les choses aromatiques.
An sa waɗansu su lura da kayayyakin da kuma dukan waɗansu kayan wuri mai tsarki, da kuma gari da ruwan inabi, da mai, turare da kuma kayan yaji.
30 Mais ceux qui faisaient les parfums des choses aromatiques, étaient des enfants des Sacrificateurs.
Amma waɗansu firistoci ne suke harhaɗa kayan yajin.
31 Et Mattitia, d'entre les Lévites, premier-né de Sallum, Corite, avait la charge de ce qui se faisait avec les plaques.
Wani Balawe mai suna Mattitiya, ɗan farin Shallum mutumin Kora ne aka danƙa masa hakkin toya burodin miƙawa.
32 Et il y en avait d'entre les enfants des Kéhathites, leurs frères, qui avaient la charge du pain de proposition pour l'apprêter chaque Sabbat.
Waɗansu’yan’uwansu Kohatawa ne suke lura da shiryawa burodin da ake kaiwa a tebur a kowane Asabbaci.
33 Et d'entr'eux il y avait aussi des chantres, chefs des pères des Lévites, qui demeuraient dans les chambres, sans avoir autre charge, parce qu'ils devaient être en fonction le jour et la nuit.
Waɗanda suke mawaƙa, kawunan iyalan Lawiyawa, sukan zauna a ɗakunan haikali kuma ba sa yin waɗansu ayyuka domin su suke da hakkin aiki dare da rana.
34 Ce sont là les chefs des pères des Lévites, selon leurs familles; ils furent chefs, et ils habitèrent à Jérusalem.
Dukan waɗannan su ne kawunan iyalan Lawiyawa, manya kamar yadda aka lissafta su a zuriyarsu, kuma suna zama a Urushalima.
35 Or Jéhiël, le père de Gabaon, habita à Gabaon; et le nom de sa femme était Mahaca.
Yehiyel mahaifin Gibeyon ya zauna a Gibeyon. Matarsa ita ce Ma’aka
36 Et son fils premier-né Habdon, puis Tsur, Kis, Bahal, Ner, Nadab,
ɗansa na fari kuwa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba’al, Ner, Nadab,
37 Guédor, Ahio, Zacharie, et Mikloth.
Gedor, Ahiyo, Zakariya da Miklot.
38 Et Mikloth engendra Siméam; et ils habitèrent vis-à-vis de leurs frères à Jérusalem avec leurs frères.
Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Su ma sun zauna kusa da danginsu a Urushalima.
39 Et Ner engendra Kis, et Kis engendra Saül, et Saül engendra Jonathan, Malki-suah, Abinadab et Esbahal.
Ner shi mahaifin Kish, Kish mahaifin Shawulu, kuma Shawulu shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab da Esh-Ba’al.
40 Et le fils de Jonathan [fut] Mérib-bahal; et Mérib-bahal engendra Mica.
Ɗan Yonatan shi ne, Merib-Ba’al wanda shi ne mahaifin Mika.
41 Et les enfants de Mica furent, Pithon, Mélec, Tahréah, [et Achaz].
’Ya’yan Mika maza su ne, Fiton, Melek, Tareya da Ahaz.
42 Et Achaz engendra Jahra; et Jahra engendra Halemeth, Hazmaveth, et Zimri; et Zimri engendra Motsa,
Ahaz shi ne mahaifin Yada, Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmawet da Zimri, Zimri kuwa shi ne mahaifin Moza.
43 Et Motsa engendra Binha, qui eut pour fils Réphaja, qui eut pour fils Elhasa, qui eut pour fils Atsel.
Moza shi ne mahaifin Bineya; Refahiya, Eleyasa da kuma Azel.
44 Et Atsel eut six fils, dont les noms [sont] Hazrikam, Bocru, Ismaël, Séharia, Hobadia, et Hanan. Ce furent là les fils d'Atsel.
Azel yana da’ya’ya maza shida, kuma ga sunayensu. Azrikam, Bokeru, Ishmayel, Sheyariya, Obadiya da Hanan. Waɗannan su ne’ya’yan Azel maza.