< 1 Chroniques 15 >

1 Or [David] bâtit pour lui des maisons dans la Cité de David, et prépara un lieu pour l'Arche de Dieu; et lui tendit un tabernacle.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Et David dit: L'Arche de Dieu ne doit être portée que par les Lévites; car l'Eternel les a choisis pour porter l'Arche de Dieu, et pour faire le service à toujours.
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 David donc assembla tous ceux d'Israël à Jérusalem, pour amener l'Arche de l'Eternel dans le lieu qu'il lui avait préparé.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 David assembla aussi les enfants d'Aaron, et les Lévites.
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 Des enfants de Kéhath, Uriël le Chef, et ses frères, six vingts.
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 Des enfants de Mérari, Hasaïa le Chef, et ses frères, deux cent et vingt.
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 Des enfants de Guersom, Joël le Chef, et ses frères, cent trente.
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 Des enfants d'Elitsaphan, Sémahja le chef, et ses frères, deux cents.
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 Des enfants de Hébron, Eliël le Chef, et ses frères, quatre-vingts.
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 Des enfants de Huziël, Hamminadab le Chef et ses frères, cent et douze.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 David donc appela Tsadoc et Abiathar les Sacrificateurs, et ces Lévites-là, [savoir], Uriël, Hasaïa, Joël, Sémahja, Eliël, et Hamminadab;
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 Et il leur dit: Vous qui êtes les Chefs des pères des Lévites, sanctifiez-vous, vous et vos frères; et transportez l'Arche de l'Eternel le Dieu d'Israël, au lieu que je lui ai préparé.
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 Parce que vous n'y avez pas été la première fois, l'Eternel notre Dieu a fait une brèche entre nous; car nous ne l'avons pas recherché comme il est ordonné.
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 Les Sacrificateurs donc et les Lévites se sanctifièrent pour amener l'Arche de l'Eternel, le Dieu d'Israël.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 Et les enfants des Lévites portèrent l'Arche de Dieu sur leurs épaules, avec les barres qu'ils avaient sur eux, comme Moïse l'avait commandé suivant la parole de l'Eternel.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 Et David dit aux Chefs des Lévites, d'établir quelques-uns de leurs frères qui chantassent avec des instruments de musique, [savoir] des musettes, des violons, et des cymbales, [et] qui fissent retentir leur voix avec joie.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 Les Lévites donc établirent Héman fils de Joël, et d'entre ses frères, Asaph fils de Bérécia; et des enfants de Mérari, qui étaient leurs frères, Ethan fils de Kusaïa;
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 Et avec eux leurs frères pour être au second rang, Zacharie, Ben, Jahaziël, Sémiramoth, Jéhiël, Hunni, Eliab, Bénéja, Mahaséïa, Mattitia, et Eliphaléhu, Miknéïa, Hobed-Edom, et Jéhiël, portiers.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 Et quant à Héman, Asaph, et Ethan chantres, [ils sonnaient] des cymbales d'airain, en faisant retentir [leur voix].
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 Et Zacharie, Haziël, Sémiramoth, Jéhiël, Hunni, Eliab, Mahaséïa, et Bénéja jouaient de la musette, sur Halamoth.
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 Et Mattitia, Eliphaléhu, Miknéja, Hobed-Edom, Jéhiël, [et] Hazaria jouaient des violons sur l'octave, pour renforcer le ton.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 Mais Kénaïa, le principal des Lévites avait la charge de faire porter l'Arche, enseignant comment il la fallait porter; car il était homme fort intelligent.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 Et Bérécia et Elkana, étaient portiers pour l'Arche.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 Et Sébania, Jéhosaphat, Nathanaël, Hamasaï, Zacharie, Bénéja, Elihézer, Sacrificateurs, sonnaient des trompettes devant l'Arche de Dieu, et Hobed-Edom et Jéhïa étaient portiers pour l'Arche.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 David donc et les Anciens d'Israël, avec les Gouverneurs de milliers, marchaient, amenant avec joie l'Arche de l'alliance de l'Eternel, de la maison d'Hobed-Edom.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 Et selon que Dieu soulageait les Lévites qui portaient l'Arche de l'alliance de l'Eternel, on sacrifiait sept veaux et sept béliers.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 Et David était vêtu d'un éphod de fin lin; et tous les Lévites aussi qui portaient l'Arche, et les chantres; et Kénaïa, qui avait la principale charge de faire porter l'Arche, était avec les chantres; et David avait un éphod de lin.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 Ainsi tout Israël amena l'Arche de l'alliance de l'Eternel, avec de grands cris de joie, et au son du cor, des trompettes et des cymbales, faisant retentir [leur voix] avec des musettes et des violons.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 Mais il arriva, comme l'Arche de l'alliance de l'Eternel entrait dans la Cité de David, que Mical fille de Saül, regardant par la fenêtre, vit le Roi David sautant et jouant, et elle le méprisa dans son cœur.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.

< 1 Chroniques 15 >