< 1 Chroniques 11 >
1 Et tous ceux d'Israël s'assemblèrent auprès de David à Hébron, et [lui] dirent: Voici, nous sommes tes os, et ta chair.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 Et même ci-devant, quand Saül était Roi, tu étais celui qui menais et qui ramenais Israël. Et l'Eternel ton Dieu t'a dit: Tu paîtras mon peuple d'Israël, et tu seras le Conducteur de mon peuple d'Israël.
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 Tous les Anciens donc d'Israël vinrent vers le Roi à Hébron; et David traita alliance avec eux à Hébron devant l'Eternel; et ils oignirent David pour Roi sur Israël, suivant la parole que l'Eternel avait proférée par le moyen de Samuël.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 Or David et tous ceux d'Israël s'en allèrent à Jérusalem, qui est Jébus; car là étaient encore les Jébusiens qui habitaient au pays.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 Et ceux qui habitaient à Jébus, dirent à David: Tu n'entreras point ici. Mais David prit la forteresse de Sion, qui est la Cité de David.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 Car David avait dit: Quiconque aura le premier frappé les Jébusiens, sera Chef et Capitaine. Et Joab fils de Tséruiä monta le premier, et fut fait Chef.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 Et David habita dans la forteresse; c'est pourquoi on l'appela la Cité de David.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 Il bâtit aussi la ville tout alentour, depuis Millo jusqu'aux environs; mais Joab répara le reste de la ville.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 Et David allait toujours en avançant et en croissant; car l'Eternel des armées était avec lui.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Ce sont ici les principaux des hommes forts que David avait, qui se portèrent vaillamment avec lui, [et] avec tout Israël, pour son Royaume, afin de le faire régner suivant la parole de l'Eternel touchant Israël.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 Ceux-ci donc sont du nombre des hommes forts que David avait; Jasobham fils de Hacmoni, Chef entre les trois principaux, qui lançant sa hallebarde contre trois cents hommes, les blessa à mort en une seule fois.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 Après lui était Eléazar fils de Dodo Ahohite, qui fut un des trois hommes forts.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 Ce fut lui qui se trouva avec David à Pasdammim, lorsque les Philistins s'étaient assemblés pour combattre; or il y avait une partie d'un champ semée d'orge, et le peuple s'en était fui devant les Philistins.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 Et eux s'arrêtèrent au milieu de cette partie du champ, et la garantirent, et battirent les Philistins. Ainsi l'Eternel accorda une grande délivrance.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Il en descendit encore trois d'entre les trente Capitaines près du rocher, vers David, en la caverne de Hadullam, lorsque l'armée des Philistins était campée dans la vallée des Réphaïms.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 Et David était alors dans la forteresse, et la garnison des Philistins était en ce même temps-là à Bethléhem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 Et David fit un souhait, et dit: Qui est-ce qui me ferait boire de l'eau du puits qui est à la porte de Bethléhem?
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 Alors ces trois hommes passèrent tout au travers du camp des Philistins, et puisèrent de l'eau du puits qui était à la porte de Bethléhem; et l'ayant apportée, la présentèrent à David, qui n'en voulut point boire, mais la répandit à l'honneur de l'Eternel.
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 Car il dit: A Dieu ne plaise que je fasse une telle chose! Boirais-je le sang de ces hommes [qui ont fait un tel voyage] au péril de leur vie; car ils m'ont apporté cette eau au péril de leur vie; ainsi il n'en voulut point boire. Ces trois vaillants hommes firent cette action-là.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Et Abisaï frère de Joab était Chef des trois, lequel lançant sa hallebarde contre trois cents hommes, les blessa à mort, et il fut célèbre entre les trois.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Entre les trois il fut plus honoré que les deux autres, et il fut leur Chef; cependant il n'égala point ces trois autres.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Bénéja aussi fils de Jéhojadah, fils d'un vaillant homme de Kabtséël, avait fait de grands exploits. Il tua deux des plus puissants hommes de Moab; et il descendit et frappa un lion au milieu d'une fosse, en un jour de neige.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 Il tua aussi un homme Egyptien qui était haut de cinq coudées. Cet Egyptien avait en sa main une hallebarde [grosse] comme une ensuble de tisserand; mais il descendit contre lui avec un bâton, et arracha la hallebarde de la main de l'Egyptien, et le tua de sa propre hallebarde.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Bénéja fils de Jéhojadah fit ces choses-là, et fut célèbre entre ces trois vaillants hommes.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Voilà, il était honoré plus que les trente; cependant il n'égala point ces trois-là; et David l'établit sur ses gens de commandement.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 Et les plus vaillants d'entre les gens de guerre furent, Hazaël, frère de Joab; et Elhanan fils de Dodo, de Bethléhem,
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Sammoth Harorite, Helets Pelonien,
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Hira fils de Hikkes Tékohite, Abihézer Hanathothite,
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbécaï Husathite, Hilaï Ahohite,
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharaï Nétophathite, Héled fils de Bahana Nétophathite,
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithaï fils de Ribaï, de Guibha des enfants de Benjamin, Bénéja Pirhathonite,
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Huraï des vallées de Gahas, Abiël Harbathite,
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Hazmaveth Baharumite, Eliachba Sahalbonite,
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 Des enfants de Hasen Guizonite, Jonathan fils de Sagué Hararite,
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam fils de Sacar Hararite, Eliphal fils d'Ur,
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hépher Mékérathite, Ahija Pélonien,
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hetsro de Carmel, Naharaï fils d'Ezbaï,
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joël frère de Nathan, Mibhar fils de Hagri,
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Tselek Hammonite, Naharaï Bérothite, qui portait les armes de Joab fils de Tséruiä,
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Hira Jithrite, Gareb Jithrite,
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Urie Héthien, Zabad fils d'Ahlaï,
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Hadina fils de Siza Rubénite, Chef des Rubénites, et trente avec lui.
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan fils de Mahaca, et Josaphat Mithnite,
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Huzija Hastérathite, Samah et Jéhiël fils de Hotham Harohérite,
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jédihaël fils de Simri, et Joha son frère, Titsite,
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliël Hammahavim, Jéribaï, et Josavia enfants d'Elnaham, et Jithma Moabite,
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliël, et Hobed, et Jasiël de Metsobaja.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.