< Psaumes 67 >

1 Au chef des chantres. Avec instruments à cordes. Psaume. Cantique. Que Dieu ait pitié de nous et qu’il nous bénisse, Qu’il fasse luire sur nous sa face, (Pause)
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Tare da kayan kiɗi masu tsirkiya. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă yi mana alheri yă kuma albarkace mu yă kuma sa fuskarsa ta haskaka a kanmu, (Sela)
2 Afin que l’on connaisse sur la terre ta voie, Et parmi toutes les nations ton salut!
don a san hanyoyinka a duniya, cetonka kuma a cikin dukan al’ummai.
3 Les peuples te louent, ô Dieu! Tous les peuples te louent.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
4 Les nations se réjouissent et sont dans l’allégresse; Car tu juges les peuples avec droiture, Et tu conduis les nations sur la terre. (Pause)
Bari al’ummai su yi murna su kuma rera don farin ciki, gama kana mulkin mutanenka da adalci kana kuma bi da al’umman duniya. (Sela)
5 Les peuples te louent, ô Dieu! Tous les peuples te louent.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
6 La terre donne ses produits; Dieu, notre Dieu, nous bénit.
Sa’an nan ƙasa za tă ba da girbinta Allah kuma, Allahnmu, zai albarkace mu.
7 Dieu, nous bénit, Et toutes les extrémités de la terre le craignent.
Allah yă sa mana albarka, dukan iyakar duniya kuma su ji tsoronsa.

< Psaumes 67 >