< Psaumes 30 >

1 Psaume. Cantique pour la dédicace de la maison. De David. Je t’exalte, ô Éternel, car tu m’as relevé, Tu n’as pas voulu que mes ennemis se réjouissent à mon sujet.
Zabura ce. Wata waƙa. Don keɓewar haikali. Ta Dawuda. Zan girmama ka Ya Ubangiji, gama ka tsamo ni daga zurfafa ba ka bar abokan gābana sun yi farin ciki a kaina ba.
2 Éternel, mon Dieu! J’ai crié à toi, et tu m’as guéri.
Ya Ubangiji Allahna, na yi kira gare ka don taimako ka kuwa warkar da ni.
3 Éternel! Tu as fait remonter mon âme du séjour des morts, Tu m’as fait revivre loin de ceux qui descendent dans la fosse. (Sheol h7585)
Ya Ubangiji, ka dawo da ni daga kabari; ka kiyaye ni daga gangarawa zuwa cikin rami. (Sheol h7585)
4 Chantez à l’Éternel, vous qui l’aimez, Célébrez par vos louanges sa sainteté!
Ku rera ga Ubangiji, ku tsarkakansa; ku yabi sunansa mai tsarki.
5 Car sa colère dure un instant, Mais sa grâce toute la vie; Le soir arrivent les pleurs, Et le matin l’allégresse.
Gama fushinsa na ɗan lokaci ne amma alherinsa har matuƙa ne; mai yiwuwa a yi kuka da dare amma farin ciki kan zo da safe.
6 Je disais dans ma sécurité: Je ne chancellerai jamais!
Sa’ad da nake lafiya, na ce, “Ba zan jijjigu ba.”
7 Éternel! Par ta grâce tu avais affermi ma montagne… Tu cachas ta face, et je fus troublé.
Ya Ubangiji, sa’ad da ka yi mini alheri, ka sa katangar dutsena ya tsaya daram; amma sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai in cika da tsoro.
8 Éternel! J’ai crié à toi, J’ai imploré l’Éternel:
A gare ka, ya Ubangiji, na yi kira; a gare ka Ubangiji na yi kukan neman jinƙai.
9 Que gagnes-tu à verser mon sang, A me faire descendre dans la fosse? La poussière a-t-elle pour toi des louanges? Raconte-t-elle ta fidélité?
“Wace riba ce a hallakata, a kuma gangarawa ta zuwa cikin rami? Ƙura za tă yabe ka ne? Za tă iya yin shelar amincinka?
10 Écoute, Éternel, aie pitié de moi! Éternel, secours-moi!
Ka ji, ya Ubangiji, ka kuwa yi mini jinƙai; Ya Ubangiji, ka zama taimakona.”
11 Et tu as changé mes lamentations en allégresse, Tu as délié mon sac, et tu m’as ceint de joie,
Ka mai da kukata ta zama rawa; ka tuɓe rigar makokina ka sa mini na farin ciki,
12 Afin que mon cœur te chante et ne soit pas muet. Éternel, mon Dieu! Je te louerai toujours.
don zuciyata za tă iya rera gare ka ba kuwa za tă yi shiru ba. Ya Ubangiji Allahna, zan yi maka godiya har abada.

< Psaumes 30 >