< Psaumes 112 >

1 Louez l’Éternel! Heureux l’homme qui craint l’Éternel, Qui trouve un grand plaisir à ses commandements.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Sa postérité sera puissante sur la terre, La génération des hommes droits sera bénie.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Il a dans sa maison bien-être et richesse, Et sa justice subsiste à jamais.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 La lumière se lève dans les ténèbres pour les hommes droits, Pour celui qui est miséricordieux, compatissant et juste.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Heureux l’homme qui exerce la miséricorde et qui prête, Qui règle ses actions d’après la justice!
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Car il ne chancelle jamais; La mémoire du juste dure toujours.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Il ne craint point les mauvaises nouvelles; Son cœur est ferme, confiant en l’Éternel.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 Son cœur est affermi; il n’a point de crainte, Jusqu’à ce qu’il mette son plaisir à regarder ses adversaires.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Il fait des largesses, il donne aux indigents; Sa justice subsiste à jamais; Sa tête s’élève avec gloire,
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 Le méchant le voit et s’irrite, Il grince les dents et se consume; Les désirs des méchants périssent.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Psaumes 112 >