< Psaumes 109 >
1 Au chef des chantres. De David. Psaume. Dieu de ma louange, ne te tais point!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Car ils ouvrent contre moi une bouche méchante et trompeuse, Ils me parlent avec une langue mensongère,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 Ils m’environnent de discours haineux Et ils me font la guerre sans cause.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Tandis que je les aime, ils sont mes adversaires; Mais moi je recours à la prière.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Ils me rendent le mal pour le bien, Et de la haine pour mon amour.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Place-le sous l’autorité d’un méchant, Et qu’un accusateur se tienne à sa droite!
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Quand on le jugera, qu’il soit déclaré coupable, Et que sa prière passe pour un péché!
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Que ses jours soient peu nombreux, Qu’un autre prenne sa charge!
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Que ses enfants deviennent orphelins, Et sa femme veuve!
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Que ses enfants soient vagabonds et qu’ils mendient, Qu’ils cherchent du pain loin de leur demeure en ruines!
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Que le créancier s’empare de tout ce qui est à lui, Et que les étrangers pillent le fruit de son travail!
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Que nul ne conserve pour lui de l’affection, Et que personne n’ait pitié de ses orphelins!
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Que ses descendants soient exterminés, Et que leur nom s’éteigne dans la génération suivante!
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Que l’iniquité de ses pères reste en souvenir devant l’Éternel, Et que le péché de sa mère ne soit point effacé!
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Qu’ils soient toujours présents devant l’Éternel, Et qu’il retranche de la terre leur mémoire,
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Parce qu’il ne s’est pas souvenu d’exercer la miséricorde, Parce qu’il a persécuté le malheureux et l’indigent, Jusqu’à faire mourir l’homme au cœur brisé!
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Il aimait la malédiction: qu’elle tombe sur lui! Il ne se plaisait pas à la bénédiction: qu’elle s’éloigne de lui!
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Qu’il revête la malédiction comme son vêtement, Qu’elle pénètre comme de l’eau dans son intérieur, Comme de l’huile dans ses os!
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Qu’elle lui serve de vêtement pour se couvrir, De ceinture dont il soit toujours ceint!
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Tel soit, de la part de l’Éternel, le salaire de mes ennemis, Et de ceux qui parlent méchamment de moi!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Et toi, Éternel, Seigneur! Agis en ma faveur à cause de ton nom, Car ta bonté est grande; délivre-moi!
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Je suis malheureux et indigent, Et mon cœur est blessé au-dedans de moi.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Je m’en vais comme l’ombre à son déclin, Je suis chassé comme la sauterelle.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Mes genoux sont affaiblis par le jeûne, Et mon corps est épuisé de maigreur.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Je suis pour eux un objet d’opprobre; Ils me regardent, et secouent la tête.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Secours-moi, Éternel, mon Dieu! Sauve-moi par ta bonté!
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 Et qu’ils sachent que c’est ta main, Que c’est toi, Éternel, qui l’as fait!
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 S’ils maudissent, toi tu béniras; S’ils se lèvent, ils seront confus, Et ton serviteur se réjouira.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Que mes adversaires revêtent l’ignominie, Qu’ils se couvrent de leur honte comme d’un manteau!
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Je louerai de ma bouche hautement l’Éternel, Je le célébrerai au milieu de la multitude;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 Car il se tient à la droite du pauvre, Pour le délivrer de ceux qui le condamnent.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.