< Proverbes 8 >

1 La sagesse ne crie-t-elle pas? L’intelligence n’élève-t-elle pas sa voix?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 C’est au sommet des hauteurs près de la route, C’est à la croisée des chemins qu’elle se place;
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 A côté des portes, à l’entrée de la ville, A l’intérieur des portes, elle fait entendre ses cris:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 Hommes, c’est à vous que je crie, Et ma voix s’adresse aux fils de l’homme.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Stupides, apprenez le discernement; Insensés, apprenez l’intelligence.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Écoutez, car j’ai de grandes choses à dire, Et mes lèvres s’ouvrent pour enseigner ce qui est droit.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Car ma bouche proclame la vérité, Et mes lèvres ont en horreur le mensonge;
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Toutes les paroles de ma bouche sont justes, Elles n’ont rien de faux ni de détourné;
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Toutes sont claires pour celui qui est intelligent, Et droites pour ceux qui ont trouvé la science.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Préférez mes instructions à l’argent, Et la science à l’or le plus précieux;
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Car la sagesse vaut mieux que les perles, Elle a plus de valeur que tous les objets de prix.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Moi, la sagesse, j’ai pour demeure le discernement, Et je possède la science de la réflexion.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 La crainte de l’Éternel, c’est la haine du mal; L’arrogance et l’orgueil, la voie du mal, Et la bouche perverse, voilà ce que je hais.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 Le conseil et le succès m’appartiennent; Je suis l’intelligence, la force est à moi.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Par moi les rois règnent, Et les princes ordonnent ce qui est juste;
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Par moi gouvernent les chefs, Les grands, tous les juges de la terre.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 J’aime ceux qui m’aiment, Et ceux qui me cherchent me trouvent.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Avec moi sont la richesse et la gloire, Les biens durables et la justice.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Mon fruit est meilleur que l’or, que l’or pur, Et mon produit est préférable à l’argent.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Je marche dans le chemin de la justice, Au milieu des sentiers de la droiture,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 Pour donner des biens à ceux qui m’aiment, Et pour remplir leurs trésors.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 L’Éternel m’a créée la première de ses œuvres, Avant ses œuvres les plus anciennes.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 J’ai été établie depuis l’éternité, Dès le commencement, avant l’origine de la terre.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Je fus enfantée quand il n’y avait point d’abîmes, Point de sources chargées d’eaux;
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Avant que les montagnes soient affermies, Avant que les collines existent, je fus enfantée;
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Il n’avait encore fait ni la terre, ni les campagnes, Ni le premier atome de la poussière du monde.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Lorsqu’il disposa les cieux, j’étais là; Lorsqu’il traça un cercle à la surface de l’abîme,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 Lorsqu’il fixa les nuages en haut, Et que les sources de l’abîme jaillirent avec force,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 Lorsqu’il donna une limite à la mer, Pour que les eaux n’en franchissent pas les bords, Lorsqu’il posa les fondements de la terre,
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 J’étais à l’œuvre auprès de lui, Et je faisais tous les jours ses délices, Jouant sans cesse en sa présence,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Jouant sur le globe de sa terre, Et trouvant mon bonheur parmi les fils de l’homme.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Et maintenant, mes fils, écoutez-moi, Et heureux ceux qui observent mes voies!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Écoutez l’instruction, pour devenir sages, Ne la rejetez pas.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Heureux l’homme qui m’écoute, Qui veille chaque jour à mes portes, Et qui en garde les poteaux!
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Car celui qui me trouve a trouvé la vie, Et il obtient la faveur de l’Éternel.
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Mais celui qui pèche contre moi nuit à son âme; Tous ceux qui me haïssent aiment la mort.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbes 8 >