< Proverbes 5 >

1 Mon fils, sois attentif à ma sagesse, Prête l’oreille à mon intelligence,
Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
2 Afin que tu conserves la réflexion, Et que tes lèvres gardent la connaissance.
don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
3 Car les lèvres de l’étrangère distillent le miel, Et son palais est plus doux que l’huile;
Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
4 Mais à la fin elle est amère comme l’absinthe, Aiguë comme un glaive à deux tranchants.
amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
5 Ses pieds descendent vers la mort, Ses pas atteignent le séjour des morts. (Sheol h7585)
Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol h7585)
6 Afin de ne pas considérer le chemin de la vie, Elle est errante dans ses voies, elle ne sait où elle va.
Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
7 Et maintenant, mes fils, écoutez-moi, Et ne vous écartez pas des paroles de ma bouche.
Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
8 Éloigne-toi du chemin qui conduit chez elle, Et ne t’approche pas de la porte de sa maison,
Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
9 De peur que tu ne livres ta vigueur à d’autres, Et tes années à un homme cruel;
don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
10 De peur que des étrangers ne se rassasient de ton bien, Et du produit de ton travail dans la maison d’autrui;
don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
11 De peur que tu ne gémisses, près de ta fin, Quand ta chair et ton corps se consumeront,
A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
12 Et que tu ne dises: Comment donc ai-je pu haïr la correction, Et comment mon cœur a-t-il dédaigné la réprimande?
Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
13 Comment ai-je pu ne pas écouter la voix de mes maîtres, Ne pas prêter l’oreille à ceux qui m’instruisaient?
Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
14 Peu s’en est fallu que je n’aie éprouvé tous les malheurs Au milieu du peuple et de l’assemblée.
Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
15 Bois les eaux de ta citerne, Les eaux qui sortent de ton puits.
Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
16 Tes sources doivent-elles se répandre au-dehors? Tes ruisseaux doivent ils couler sur les places publiques?
In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
17 Qu’ils soient pour toi seul, Et non pour des étrangers avec toi.
Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
18 Que ta source soit bénie, Et fais ta joie de la femme de ta jeunesse,
Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
19 Biche des amours, gazelle pleine de grâce: Sois en tout temps enivré de ses charmes, Sans cesse épris de son amour.
Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
20 Et pourquoi, mon fils, serais-tu épris d’une étrangère, Et embrasserais-tu le sein d’une inconnue?
Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
21 Car les voies de l’homme sont devant les yeux de l’Éternel, Qui observe tous ses sentiers.
Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
22 Le méchant est pris dans ses propres iniquités, Il est saisi par les liens de son péché.
Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
23 Il mourra faute d’instruction, Il chancellera par l’excès de sa folie.
Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.

< Proverbes 5 >