< Proverbes 22 >
1 La réputation est préférable à de grandes richesses, Et la grâce vaut mieux que l’argent et que l’or.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 Le riche et le pauvre se rencontrent; C’est l’Éternel qui les a faits l’un et l’autre.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 L’homme prudent voit le mal et se cache, Mais les simples avancent et sont punis.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 Le fruit de l’humilité, de la crainte de l’Éternel, C’est la richesse, la gloire et la vie.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Des épines, des pièges sont sur la voie de l’homme pervers; Celui qui garde son âme s’en éloigne.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Instruis l’enfant selon la voie qu’il doit suivre; Et quand il sera vieux, il ne s’en détournera pas.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 Le riche domine sur les pauvres, Et celui qui emprunte est l’esclave de celui qui prête.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 Celui qui sème l’iniquité moissonne l’iniquité, Et la verge de sa fureur disparaît.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 L’homme dont le regard est bienveillant sera béni, Parce qu’il donne de son pain au pauvre.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Chasse le moqueur, et la querelle prendra fin; Les disputes et les outrages cesseront.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 Celui qui aime la pureté du cœur, Et qui a la grâce sur les lèvres, a le roi pour ami.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 Les yeux de l’Éternel gardent la science, Mais il confond les paroles du perfide.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 Le paresseux dit: Il y a un lion dehors! Je serai tué dans les rues!
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 La bouche des étrangères est une fosse profonde; Celui contre qui l’Éternel est irrité y tombera.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 La folie est attachée au cœur de l’enfant; La verge de la correction l’éloignera de lui.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 Opprimer le pauvre pour augmenter son bien, C’est donner au riche pour n’arriver qu’à la disette.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Prête l’oreille, et écoute les paroles des sages; Applique ton cœur à ma science.
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 Car il est bon que tu les gardes au-dedans de toi, Et qu’elles soient toutes présentes sur tes lèvres.
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 Afin que ta confiance repose sur l’Éternel, Je veux t’instruire aujourd’hui, oui, toi.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 N’ai-je pas déjà pour toi mis par écrit Des conseils et des réflexions,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 Pour t’enseigner des choses sûres, des paroles vraies, Afin que tu répondes par des paroles vraies à celui qui t’envoie?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 Ne dépouille pas le pauvre, parce qu’il est pauvre, Et n’opprime pas le malheureux à la porte;
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 Car l’Éternel défendra leur cause, Et il ôtera la vie à ceux qui les auront dépouillés.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 Ne fréquente pas l’homme colère, Ne va pas avec l’homme violent,
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 De peur que tu ne t’habitues à ses sentiers, Et qu’ils ne deviennent un piège pour ton âme.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 Ne sois pas parmi ceux qui prennent des engagements, Parmi ceux qui cautionnent pour des dettes;
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 Si tu n’as pas de quoi payer, Pourquoi voudrais-tu qu’on enlève ton lit de dessous toi?
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 Ne déplace pas la borne ancienne, Que tes pères ont posée.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 Si tu vois un homme habile dans son ouvrage, Il se tient auprès des rois; Il ne se tient pas auprès des gens obscurs.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.