< Nombres 34 >

1 L’Éternel parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Donne cet ordre aux enfants d’Israël, et dis-leur: Quand vous serez entrés dans le pays de Canaan, ce pays deviendra votre héritage, le pays de Canaan, dont voici les limites.
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 Le côté du midi commencera au désert de Tsin près d’Édom. Ainsi, votre limite méridionale partira de l’extrémité de la mer Salée, vers l’orient;
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 elle tournera au sud de la montée d’Akrabbim, passera par Tsin, et s’étendra jusqu’au midi de Kadès-Barnéa; elle continuera par Hatsar-Addar, et passera vers Atsmon;
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 depuis Atsmon, elle tournera jusqu’au torrent d’Égypte, pour aboutir à la mer.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 Votre limite occidentale sera la grande mer: ce sera votre limite à l’occident.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 Voici quelle sera votre limite septentrionale: à partir de la grande mer, vous la tracerez jusqu’à la montagne de Hor;
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 depuis la montagne de Hor, vous la ferez passer par Hamath, et arriver à Tsedad;
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 elle continuera par Ziphron, pour aboutir à Hatsar-Énan: ce sera votre limite au septentrion.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 Vous tracerez votre limite orientale de Hatsar-Énan à Schepham;
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 elle descendra de Schepham vers Ribla, à l’orient d’Aïn; elle descendra, et s’étendra le long de la mer de Kinnéreth, à l’orient;
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 elle descendra encore vers le Jourdain, pour aboutir à la mer Salée. Tel sera votre pays avec ses limites tout autour.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Moïse transmit cet ordre aux enfants d’Israël, et dit: C’est là le pays que vous partagerez par le sort, et que l’Éternel a résolu de donner aux neuf tribus et à la demi-tribu.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 Car la tribu des fils de Ruben et la tribu des fils de Gad ont pris leur héritage, selon les maisons de leurs pères; la demi-tribu de Manassé a aussi pris son héritage.
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 Ces deux tribus et la demi-tribu ont pris leur héritage en deçà du Jourdain, vis-à-vis de Jéricho, du côté de l’orient.
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 L’Éternel parla à Moïse, et dit:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Voici les noms des hommes qui partageront entre vous le pays: le sacrificateur Éléazar, et Josué, fils de Nun.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 Vous prendrez encore un prince de chaque tribu, pour faire le partage du pays.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 Voici les noms de ces hommes. Pour la tribu de Juda: Caleb, fils de Jephunné;
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 pour la tribu des fils de Siméon: Samuel, fils d’Ammihud;
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 pour la tribu de Benjamin: Élidad, fils de Kislon;
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 pour la tribu des fils de Dan: le prince Buki, fils de Jogli;
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 pour les fils de Joseph, pour la tribu des fils de Manassé: le prince Hanniel, fils d’Éphod;
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 et pour la tribu des fils d’Éphraïm: le prince Kemuel, fils de Schiphtan;
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 pour la tribu des fils de Zabulon: le prince Élitsaphan, fils de Parnac;
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 pour la tribu des fils d’Issacar: le prince Paltiel, fils d’Azzan;
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 pour la tribu des fils d’Aser: le prince Ahihud, fils de Schelomi;
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 pour la tribu des fils de Nephthali: le prince Pedahel, fils d’Ammihud.
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Tels sont ceux à qui l’Éternel ordonna de partager le pays de Canaan entre les enfants d’Israël.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Nombres 34 >