< Job 18 >

1 Bildad de Schuach prit la parole et dit:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Quand mettrez-vous un terme à ces discours? Ayez de l’intelligence, puis nous parlerons.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Pourquoi sommes-nous regardés comme des bêtes? Pourquoi ne sommes-nous à vos yeux que des brutes?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 O toi qui te déchires dans ta fureur, Faut-il, à cause de toi, que la terre devienne déserte? Faut-il que les rochers disparaissent de leur place?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 La lumière du méchant s’éteindra, Et la flamme qui en jaillit cessera de briller.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 La lumière s’obscurcira sous sa tente, Et sa lampe au-dessus de lui s’éteindra.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Ses pas assurés seront à l’étroit; Malgré ses efforts, il tombera.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Car il met les pieds sur un filet, Il marche dans les mailles,
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Il est saisi au piège par le talon, Et le filet s’empare de lui;
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Le cordeau est caché dans la terre, Et la trappe est sur son sentier.
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Des terreurs l’assiègent, l’entourent, Le poursuivent par derrière.
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 La faim consume ses forces, La misère est à ses côtés.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Les parties de sa peau sont l’une après l’autre dévorées, Ses membres sont dévorés par le premier-né de la mort.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Il est arraché de sa tente où il se croyait en sûreté, Il se traîne vers le roi des épouvantements.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Nul des siens n’habite sa tente, Le soufre est répandu sur sa demeure.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 En bas, ses racines se dessèchent; En haut, ses branches sont coupées.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Sa mémoire disparaît de la terre, Son nom n’est plus sur la face des champs.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 Il est poussé de la lumière dans les ténèbres, Il est chassé du monde.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Il ne laisse ni descendants ni postérité parmi son peuple, Ni survivant dans les lieux qu’il habitait.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Les générations à venir seront étonnées de sa ruine, Et la génération présente sera saisie d’effroi.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Point d’autre destinée pour le méchant, Point d’autre sort pour qui ne connaît pas Dieu!
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”

< Job 18 >