< Ézéchiel 23 >
1 La parole de l’Éternel me fut adressée, en ces mots:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l’homme, il y avait deux femmes, Filles d’une même mère.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 Elles se sont prostituées en Égypte, Elles se sont prostituées dans leur jeunesse; Là leurs mamelles ont été pressées, Là leur sein virginal a été touché.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 L’aînée s’appelait Ohola, Et sa sœur Oholiba; Elles étaient à moi, Et elles ont enfanté des fils et des filles. Ohola, c’est Samarie; Oholiba, c’est Jérusalem.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Ohola me fut infidèle; Elle s’enflamma pour ses amants, Les Assyriens ses voisins,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 Vêtus d’étoffes teintes en bleu, Gouverneurs et chefs, Tous jeunes et charmants, Cavaliers montés sur des chevaux.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 Elle s’est prostituée à eux, A toute l’élite des enfants de l’Assyrie; Elle s’est souillée avec tous ceux pour lesquels elle s’était enflammée, Elle s’est souillée avec toutes leurs idoles.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Elle n’a pas renoncé à ses prostitutions d’Égypte: Car ils avaient couché avec elle dans sa jeunesse, Ils avaient touché son sein virginal, Et ils avaient répandu sur elle leurs prostitutions.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 C’est pourquoi je l’ai livrée entre les mains de ses amants, Entre les mains des enfants de l’Assyrie, Pour lesquels elle s’était enflammée.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Ils ont découvert sa nudité, Ils ont pris ses fils et ses filles, Ils l’ont fait périr elle-même avec l’épée; Elle a été en renom parmi les femmes, Après les jugements exercés sur elle.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 Sa sœur Oholiba vit cela, Et fut plus déréglée qu’elle dans sa passion; Ses prostitutions dépassèrent celles de sa sœur.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Elle s’enflamma pour les enfants de l’Assyrie, Gouverneurs et chefs, ses voisins, Vêtus magnifiquement, Cavaliers montés sur des chevaux, Tous jeunes et charmants.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 Je vis qu’elle s’était souillée, Que l’une et l’autre avaient suivi la même voie.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 Elle alla même plus loin dans ses prostitutions. Elle aperçut contre les murailles des peintures d’hommes, Des images de Chaldéens peints en couleur rouge,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 Avec des ceintures autour des reins, Avec des turbans de couleurs variées flottant sur la tête, Tous ayant l’apparence de chefs, Et figurant des enfants de Babylone, De la Chaldée, leur patrie;
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 Elle s’enflamma pour eux, au premier regard, Et leur envoya des messagers en Chaldée.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Et les enfants de Babylone se rendirent auprès d’elle, Pour partager le lit des amours, Et ils la souillèrent par leurs prostitutions. Elle s’est souillée avec eux, Puis son cœur s’est détaché d’eux.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Elle a mis à nu son impudicité, Elle a découvert sa nudité; Et mon cœur s’est détaché d’elle, Comme mon cœur s’était détaché de sa sœur.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Elle a multiplié ses prostitutions, En pensant aux jours de sa jeunesse, Lorsqu’elle se prostituait au pays d’Égypte.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 Elle s’est enflammée pour des impudiques, Dont la chair était comme celle des ânes, Et l’approche comme celle des chevaux.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 Tu t’es souvenue des crimes de ta jeunesse, Lorsque les Égyptiens pressaient tes mamelles, A cause de ton sein virginal.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 C’est pourquoi, Oholiba, ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Voici, j’excite contre toi tes amants, Ceux dont ton cœur s’est détaché, Et je les amène de toutes parts contre toi;
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 Les enfants de Babylone et tous les Chaldéens, Nobles, princes et seigneurs, Et tous les enfants de l’Assyrie avec eux, Jeunes et charmants, Tous gouverneurs et chefs, Chefs illustres, Tous montés sur des chevaux.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Ils marchent contre toi avec des armes, des chars et des roues, Et une multitude de peuples; Avec le grand bouclier et le petit bouclier, avec les casques, Ils s’avancent de toutes parts contre toi. Je leur remets le jugement, Et ils te jugeront selon leurs lois.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 Je répands ma colère sur toi, Et ils te traiteront avec fureur. Ils te couperont le nez et les oreilles, Et ce qui reste de toi tombera par l’épée; Ils prendront tes fils et tes filles, Et ce qui reste de toi sera dévoré par le feu.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 Ils te dépouilleront de tes vêtements, Et ils enlèveront les ornements dont tu te pares.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 Je mettrai fin à tes crimes Et à tes prostitutions du pays d’Égypte; Tu ne porteras plus tes regards vers eux, Tu ne penseras plus à l’Égypte.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 Car ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Voici, je te livre entre les mains de ceux que tu hais, Entre les mains de ceux dont ton cœur s’est détaché.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 Ils te traiteront avec haine; Ils enlèveront toutes tes richesses, Et te laisseront nue, entièrement nue; La honte de tes impudicités sera découverte, De tes crimes et de tes prostitutions.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 Ces choses t’arriveront, Parce que tu t’es prostituée aux nations, Parce que tu t’es souillée par leurs idoles.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Tu as marché dans la voie de ta sœur, Et je mets sa coupe dans ta main.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Tu boiras la coupe de ta sœur, Tu la boiras large et profonde; Elle te rendra un objet de risée et de moquerie; Elle contient beaucoup.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Tu seras remplie d’ivresse et de douleur; C’est la coupe de désolation et de destruction, La coupe de ta sœur Samarie.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Tu la boiras, tu la videras, Tu la briseras en morceaux, Et tu te déchireras le sein. Car j’ai parlé, Dit le Seigneur, l’Éternel.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 C’est pourquoi ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Parce que tu m’as oublié, Parce que tu m’as rejeté derrière ton dos, Porte donc aussi la peine de tes crimes et de tes prostitutions.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 L’Éternel me dit: Fils de l’homme, jugeras-tu Ohola et Oholiba? Déclare-leur leurs abominations!
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Elles se sont livrées à l’adultère, et il y a du sang à leurs mains: Elles ont commis adultère avec leurs idoles; Et les enfants qu’elles m’avaient enfantés, Elles les ont fait passer par le feu Pour qu’ils leur servent d’aliment.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Voici encore ce qu’elles m’ont fait: Elles ont souillé mon sanctuaire dans le même jour, Et elles ont profané mes sabbats.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 Elles ont immolé leurs enfants à leurs idoles, Et elles sont allées le même jour dans mon sanctuaire, Pour le profaner. C’est là ce qu’elles ont fait dans ma maison.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 Et même elles ont fait chercher des hommes venant de loin, Elles leur ont envoyé des messagers, et voici, ils sont venus. Pour eux tu t’es lavée, tu as mis du fard à tes yeux, Tu t’es parée de tes ornements;
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 Tu t’es assise sur un lit magnifique, Devant lequel une table était dressée, Et tu as placé sur cette table mon encens et mon huile.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 On entendait les cris d’une multitude joyeuse; Et parmi cette foule d’hommes On a fait venir du désert des Sabéens, Qui ont mis des bracelets aux mains des deux sœurs Et de superbes couronnes sur leurs têtes.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Je dis alors au sujet de celle qui a vieilli dans l’adultère: Continuera-t-elle maintenant ses prostitutions, et viendra-t-on à elle?
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 Et l’on est venu vers elle comme l’on va chez une prostituée; C’est ainsi qu’on est allé vers Ohola et Oholiba, Ces femmes criminelles.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Mais des hommes justes les jugeront, Comme on juge les femmes adultères, Comme on juge celles qui répandent le sang; Car elles sont adultères, et il y a du sang à leurs mains.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 Car ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Je ferai monter contre elles une multitude, Et je les livrerai à la terreur et au pillage.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 Cette multitude les lapidera, Et les abattra à coups d’épée; On tuera leurs fils et leurs filles, On brûlera leurs maisons par le feu.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 Je ferai cesser ainsi le crime dans le pays; Toutes les femmes recevront instruction, Et ne commettront pas de crime comme le vôtre.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 On fera retomber votre crime sur vous, Et vous porterez les péchés de vos idoles. Et vous saurez que je suis le Seigneur, l’Éternel.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”