< Ruth 2 >

1 Il y avait un homme connu de Noémi et de son époux; cet homme, parent d'Elimélech, était riche et il se nommait Booz.
To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
2 Et Ruth la Moabite dit à Noémi: Je m'en vais aux champs, et je ramasserai des épis à la suite des moissonneurs, chez celui aux yeux de qui je trouverai grâce; et Noémi répondit: Va, ma fille.
Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
3 Elle partit donc, et, étant arrivée, elle glana dans un champ, derrière les moissonneurs; elle était, tombée par aventure sur un endroit du champ de Booz, le parent d'Elimélech.
Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
4 Et voilà que Booz vint de Bethléem, et il dit aux moissonneurs: Le Seigneur soit avec vous, et ils lui dirent: Que le Seigneur te bénisse.
Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
5 Et Booz dit à son serviteur, qui était placé au-dessus des moissonneurs: Qui est cette jeune fille?
Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
6 Son serviteur, qui était placé au-dessus des moissonneurs, répondit: C'est la jeune Moabite, qui est revenue avec Noémi du champ de Moab.
Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
7 Elle m'a dit: le glanerai et je recueillerai des épis derrière les moissonneurs; et elle a glané depuis le matin jusqu'au soir, et elle n'a pas pris dans le champ un moment de repos.
Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
8 Alors, Booz dit à Ruth: N'as-tu pas entendu, ma fille? Ne va pas glaner dans un autre champ; ne t'éloigne pas d'ici, et attache-toi aux pas de mes filles.
Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
9 Les yeux fixés sur le champ où elles moissonnent, tu iras après elles; voilà que j'ai commandé à mes serviteurs de te respecter. Et quand tu auras soif, tu iras aux vaisseaux, et tu boiras où boivent mes serviteurs.
Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
10 Et, pour témoigner son respect, elle tomba la face contre terre, et elle lui dit: Comment ai-je trouvé grâce devant tes yeux pour que tu m'honores, moi qui suis une étrangère?
Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
11 Et il répondit: On m'a raconté tout ce que tu as fait pour ta belle mère après la mort de son mari, et comment tu as quitté ton père et ta mère et le lieu de ta naissance, et comment tu es venue chez un peuple qu'auparavant tu ne connaissais pas.
Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
12 Que le Seigneur rémunère ta bonne action; que le Seigneur Dieu d'Israël, à qui tu es venue pour t'abriter sous ses ailes, t'accorde un salaire abondant.
Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
13 Et elle reprit: Que je trouve, seigneur, grâce devant tes yeux, puisque tu m'as consolée, et que tu as parlé au cœur de ta servante, et je serai comme l'une de tes servantes.
Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
14 Et Booz lui dit: Voici le moment de manger, viens ici; tu mangeras du pain et tu tremperas la bouchée dans le vinaigre. Ruth s'assit donc auprès des moissonneurs, et Booz lui présenta des gâteaux de farine; elle mangea et elle fut rassasiée, et il lui en resta.
A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
15 Ensuite, elle se leva, pour glaner, et Booz donna ses ordres à ses serviteurs, disant: Laissez-la glaner au milieu des Javelles et gardez-vous de la molester.
Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
16 En apportant les épis, apportez-en pour elle, et en les jetant à terre, jetez pour elle une part de ce que vous recueillez; elle glanera, elle mangera, et vous ne lui ferez aucun reproche.
Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
17 Et elle glana jusqu'à la nuit, puis elle battit les épis qu'elle avait ramassés, et elle en tira près d'une mesure d'orge.
Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
18 Elle l'emporta et elle rentra dans la ville; sa belle-mère vit ce qu'elle avait recueilli, et Ruth lui donna les restes qu'elle avait rapportés des mets dont elle s'était rassasiée.
Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
19 Et sa belle-mère lui dit: Où as-tu glané aujourd'hui, où as-tu travaillé? Béni soit celui qui t'a accueillie. Et Ruth apprit à sa belle-mère où elle avait travaillé, et elle lui dit: L'homme chez qui j'ai glané aujourd'hui se nomme Booz.
Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
20 Et Noémi dit à sa bru: Béni soit-il, au nom du Seigneur, parce que sa miséricorde n'a manqué ni aux vivants, ni aux morts. Et Noémi ajouta: L'homme nous est proche, c'est un de nos parents.
Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
21 Et Ruth reprit: C'est sans doute pour cela qu'il m'a dit: Attache-toi aux pas de mes filles jusqu'à ce qu'elles aient achevé toute ma moisson.
Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
22 Et Noémi dit à Ruth, sa bru: Bon, mon enfant, si tu marches avec ses filles, on ne te contrariera pas dans un autre champ.
Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
23 Ruth s'attacha donc aux pas des filles de Booz pour glaner jusqu'à la fin de la moisson des orges et des froments.
Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.

< Ruth 2 >