< Psaumes 96 >
1 Quand le temple fut rebâti après la captivité, cantique de David. Chantez au Seigneur un cantique nouveau; que toute la terre chante au Seigneur!
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Chantez au Seigneur; bénissez son nom; publiez avec joie son salut de jour en jour.
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Publiez aux Gentils sa gloire, et ses merveilles à tous les peuples,
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 Car le Seigneur est grand et digne de louanges infinies; il est plus terrible que tous les dieux.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Car tous les dieux des Gentils sont des démons; mais le Seigneur a créé les cieux.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Louanges et beauté sont en sa présence; la sainteté et la majesté sont en son sanctuaire.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Tribus des Gentils, rendez au Seigneur, rendez à Dieu gloire et honneur.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Rendez gloire au Seigneur et à son nom; prenez des victimes et entrez dans ses parvis.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Adorez le Seigneur en son temple saint, et que devant sa face tremble toute la terre.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Dites aux Gentils: Le Seigneur règne, car il a affermi le globe de la terre, et il ne sera plus ébranlé; il jugera les peuples avec droiture.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Que les cieux se réjouissent et que la terre tressaille d'allégresse; que la mer en sa plénitude soit émue.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 Les champs et tout ce qu'ils renferment se réjouiront; alors tressailliront les arbres de la forêt
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 Devant la face du Seigneur; car il vient, car il vient juger la terre. Il jugera le monde selon sa justice, et les peuples selon sa vérité.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.