< Psaumes 88 >

1 Psaume des fils de Koré. Jusqu'à la Fin, sur Maeleth. Méditation d'Eman l'Israélite. Seigneur, Dieu de mon salut, j'ai crié devant toi, le jour et la nuit.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Que mon oraison pénètre en ta présence; incline ton oreille vers ma prière. Seigneur.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Car mon âme a été remplie de maux, et ma vie s'est approchée de l'enfer. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 J'ai été compté parmi ceux qui descendent dans la fosse; je suis devenu comme un homme sans secours,
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Libre parmi les morts, comme ceux qui tombent mortellement blessés, qui dorment dans le sépulcre, et dont tu ne te souviens plus; ceux-là aussi ont été repoussés par ta main.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 On m'a mis au plus profond de la fosse, dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Ta colère s'est appesantie sur moi, et tu as fait passer sur moi tous tes flots.
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Tu as éloigné de moi mes proches; ils m'ont en en abomination. J'ai été livré, et je n'ai pu sortir.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mes yeux ont été affaiblis par la misère. Et j'ai crié vers toi tout le jour. Seigneur; j'ai étendu vers toi les mains.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Feras-tu des prodiges pour les morts? ou des médecins les ressusciteront-ils, afin qu'ils te louent?
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Quelqu'un dans le sépulcre publiera-t-il ta miséricorde, ou ta vérité dans la perdition?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Dans les ténèbres, connaîtra-t-on tes merveilles? Et ta justice est-elle dans une terre oubliée?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Et moi, Seigneur, J'ai crié vers toi; et dès l'aurore ma prière te parviendra.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Pourquoi, Seigneur, rejette-tu ma prière et détournes-tu de moi ta face?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Je suis pauvre, et dans les labeurs depuis ma jeunesse; mais après avoir été exalté, j'ai été humilié et confondu.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Sur moi ont passé tes colères, et tes épouvantements m'ont troublé.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Ils m'ont entouré comme des flots; durant tout le jour, ils m'ont assiégé tous à la fois.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Tu as écarté de moi tout ami et mes proches de ma misère.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psaumes 88 >