< Psaumes 6 >

1 Jusqu'à la Fin, un psaume de David, pris des hymnes en octave. Seigneur, ne me reprends pas en ta fureur, ne me châtie pas en ta colère.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Aie pitié de moi, Seigneur, car je suis infirme; guéris-moi, Seigneur, car mes os sont bouleversés.
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 Et mon âme a été grandement troublée, et toi, jusques à quand, Seigneur?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Reviens, Seigneur, délivre mon âme; sauve-moi par ta miséricorde.
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 Car il n'est personne en la mort qui se souvienne de toi; et aux enfers, qui te rendra gloire? (Sheol h7585)
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
6 Je me suis fatigué à gémir; je laverai chaque nuit ma couche; j'arroserai mon lit de mes larmes.
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 Mon œil a été troublé par la fureur; je suis devenu vieux au milieu de tous mes ennemis.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Éloignez-vous de moi, vous tous ouvriers d'iniquité; car le Seigneur a entendu la voix de mes larmes.
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 Le Seigneur a écouté mon oraison; le Seigneur a exaucé ma prière.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Que tous mes ennemis rougissent de honte et soient troublés au fond de l'âme; qu'ils fuient soudain et soient grandement humiliés.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.

< Psaumes 6 >