< Psaumes 59 >
1 Jusqu'à la Fin, avec cette inscription de David: Ne détruis pas; quand Saül envoya et fit garder sa maison pour le mettre à mort. O Dieu, délivre-moi de mes ennemis; délivre-moi de ceux qui s'élèvent contre moi.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Délivre-moi des ouvriers d'iniquité, et sauve-moi des hommes de sang.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 Car voilà qu'ils ont fait la chasse à mon âme; des hommes puissants se sont jetés sur moi.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Ce n'est ni mon iniquité ni mon péché, Seigneur, qui en sont la cause: exempt d'iniquité, j'ai couru droit devant moi.
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 Réveille-toi, viens à mon aide, et vois, Seigneur, Dieu des vertus. Dieu d'Israël; sois attentif à visiter les nations; n'aie aucune pitié pour ceux qui commettent l'iniquité.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 Ils viendront sur le soir, et ils seront affamés comme des chiens, et ils courront autour de la ville.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Voilà qu'ils vociféreront, et ils auront une épée sur les lèvres: Qui nous entend? s'écrieront-ils.
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 Et toi, Seigneur, tu riras d'eux; tu réduiras toutes les nations à néant.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Je garderai ma force en toi; car ô mon Dieu, tu es mon défenseur.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 Quant à mon Dieu, sa miséricorde me préviendra.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 Dieu me montrera sa vengeance sur mes ennemis. Ne les fais pas mourir, de peur que ton peuple n'en perde la mémoire. Disperse-les en ta puissance, et renverse-les. Dieu mon protecteur.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 Châtie le péché de leur bouche, les paroles de leurs lèvres; qu'ils soient punis dans leur orgueil; et l'on s'entretiendra de leurs malédictions, de leurs mensonges.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Détruis-les, détruis-les en ta colère; et ils ne subsisteront plus; et l'on saura que le Dieu de Jacob règne jusqu'aux confins de la terre.
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 Ils reviendront sur le soir; ils seront affamés comme des chiens, et ils courront autour de la ville.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 Ils se disperseront pour manger; et s'ils ne sont point rassasiés, ils murmureront.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 Pour moi, je chanterai ta puissance, et, dès l'aurore, je me réjouirai de ta miséricorde; car tu es mon défenseur et mon refuge au jour de mon affliction.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 Je te chanterai mes psaumes, ô mon Sauveur, ô mon Dieu; tu es mon défenseur, mon Dieu et ma miséricorde.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.