< Psaumes 58 >
1 Jusqu'à la Fin, avec cette inscription de David: Ne détruis pas. O fils des hommes, si vous parlez sincèrement de la justice, jugez donc avec droiture.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Car vous faites en votre cœur des iniquités sur la terre, et vos mains trament l'injustice.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 Dès le sein de leur mère, les pécheurs ont dévié; à peine hors de ses entrailles, ils se sont égarés; ils ont dit des mensonges.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Leur colère est comme le venin du serpent, ou du sourd aspic, dont les oreilles sont bouchées,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 Qui n'entendra point la voix des enchanteurs, et résistera aux charmes les plus subtils.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 Dieu leur a brisé les dents dans la bouche; le Seigneur a broyé la mâchoire des lions.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Ils s'écouleront comme un flot qui passe; le Seigneur tiendra son arc tendu contre eux, jusqu'à ce qu'ils aient péri.
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Ils seront réduits à rien, comme la cire qui se fond; le feu est tombé sur eux, ils n'ont plus vu le soleil.
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Avant que vos épines approchent de la hauteur d'un arbrisseau, le Seigneur vous dévorera même pleins de vie, dans l'excès de sa colère.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Le juste se réjouira, lorsqu'il verra la punition des impies; il se lavera les mains dans le sang des pécheurs.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Et l'on dira: Puisqu'il y a des fruits pour les justes, il est donc un Dieu qui les juge sur la terre.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”