< Psaumes 51 >
1 Jusqu'à la Fin. Psaume de David. Quand le prophète Nathan le vint trouver, parce qu'il avait eu commerce avec Bersabée. Aie pitié de moi, Seigneur, selon ta grande miséricorde; et selon l'immensité de ta compassion, efface mon iniquité.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Lave-moi de plus en plus de mon crime, et purifie-moi de mon péché.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 Car je connais mon iniquité, et mon péché est toujours devant ma face.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 C'est contre toi seul que j'ai péché, et devant toi que j'ai fait le mal; tu l'as permis, afin que tu sois reconnu juste dans tes paroles et que tu triomphes dans tes jugements.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Car voilà que j'ai été conçu dans l'iniquité, et ma mère m'a conçu dans le péché.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Mais toi; tu aimes la vérité, et tu m'as révélé les choses obscures et profondes de ta sagesse.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Tu m'aspergeras avec l'hysope, et je serai purifié; tu me laveras, et je serai plus blanc que la neige.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Tu me feras entendre la joie et l'allégresse, et mes os affligés se réjouiront.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Détourne ta face de tous mes péchés, et efface toutes mes iniquités.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Crée en moi un cœur pur, ô mon Dieu, et rétablis un esprit droit en mes entrailles.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Ne me rejette pas de ta présence, et ne retire pas de moi ton Esprit- Saint.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Rends-moi la joie de ton salut, et raffermis-moi en me donnant l'Esprit de force.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 J'enseignerai tes voies aux méchants, et les impies se convertiront à toi.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Lave-moi du sang versé, ô Dieu, Dieu de mon salut, et ma langue se réjouira de ta justice.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Seigneur, tu ouvriras mes lèvres, et ma bouche proclamera tes louanges.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 Car si tu avais voulu un sacrifice, je te l'aurais offert; mais les holocaustes ne te sont point agréables.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 Le sacrifice qui plaît à Dieu est un esprit contrit; Dieu ne méprisera pas un cœur contrit et humilié.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Seigneur, fais en ta bonté, pour Sion, que les remparts de Jérusalem soient édifiés.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Alors tu agréeras un sacrifice de justice, des oblations et des holocaustes; alors on offrira des veaux sur ton autel.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.