< Psaumes 50 >

1 Psaume d'Asaph. Le Dieu des dieux, le Seigneur a parlé, et il a appelé la terre depuis l'Orient jusqu'à l'Occident
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 De Sion vient la splendeur de sa beauté.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Dieu, notre Dieu viendra manifestement, et ne gardera pas le silence; un feu sera allume en sa présence, et tout alentour un vent impétueux soufflera.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Il convoquera le ciel et la terre, pour juger son peuple.
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Amenez-lui ses saints, ceux qui ont fait alliance avec lui, pour les sacrifices.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Et les cieux annonceront sa justice; car Dieu est le juge.
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Écoute, mon peuple, et je parlerai; Israël, je te l'atteste: je suis Dieu, je suis ton Dieu.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Je ne te réprimanderai point sur tes sacrifices; car tes holocaustes sont toujours devant mes yeux.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Je ne prendrai pas de bœufs de ta maison, ni de boucs de tes menus troupeaux.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Car toutes les bêtes de la forêt m'appartiennent, et le bétail des montagnes et les taureaux.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Je connais tous les oiseaux du ciel, et la beauté des champs est à moi.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Si j'ai faim, je ne te le dis pas; car toute la terre habitée m'appartient et sa plénitude.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Est-ce que je mange la chair des taureaux? est-ce que je bois le sang des boucs?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Immole à Dieu une victime de louanges; rends au Tout-Puissant tes vœux.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Invoque-moi au jour de l'affliction, et je te sauverai, et tu me rendras grâces.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Mais Dieu a dit au pécheur: Pourquoi publies-tu mes justices et as-tu mon alliance à la bouche,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Quand tu n'aimes point ma discipline, et que tu as rejeté loin de toi ma parole?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Si tu voyais un larron, tu courais avec lui; tu avais ta part avec les adultères;
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Ta bouche abondait en méchanceté, et ta langue tramait la fraude.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Assis, tu médisais de ton frère; tu scandalisais le fils de ta mère.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Voilà ce que tu faisais, et j'ai gardé le silence; mais tu t'imaginais faussement que je serais semblable à toi. Je te convaincrai, et je mettrai tes offenses devant ta face.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Comprenez donc ces choses, vous qui oubliez Dieu; de peur qu'un jour il ne vous ravisse, et que nul ne vous délivre.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 C'est un sacrifice de louange qui m'honore, et la voie où je montrerai le salut de Dieu.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psaumes 50 >