< Psaumes 47 >

1 Jusqu'à la Fin, psaume des fils de Koré. Nations, battez toutes des mains, chantez à Dieu d'une voix pleine d'allégresse.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Car le Seigneur est élevé; il est terrible: c'est le grand Roi de toute la terre.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Il nous a assujetti les peuples, et mis les Gentils sous nos pieds.
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Il nous a choisis pour son héritage, nous, la beauté de Jacob, qu'il aime.
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Dieu est monté au milieu de la joie; le Seigneur, au son de la trompette.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Chantez à notre Dieu; chantez à notre Roi, chantez.
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Et puisque Dieu est le roi de toute la terre, chantez avec intelligence.
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Dieu règne sur les nations; Dieu est assis sur le trône de sa sainteté.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Les princes des peuples se sont réunis avec le Dieu d'Abraham; car les puissants de la terre ont été élevés par Dieu bien au-dessus des autres hommes.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.

< Psaumes 47 >