< Psaumes 3 >

1 Psaume de David, lorsqu'il fuyait de devant son fils Absalom. Seigneur, pourquoi ceux qui m'affligent se sont-ils multipliés? Combien se soulèvent contre moi!
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 Combien disent à mon âme qu'il n'est point de salut pour elle! Interlude.
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 Mais toi, Seigneur, tu es mon appui et ma gloire; c'est toi qui relève ma tête.
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 De ma voix, j'ai crié au Seigneur, et il m'a entendu du haut de sa montagne sainte. Interlude.
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 Et je me suis endormi d'un profond sommeil; je me suis réveillé, car le Seigneur me défendra.
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 Je ne craindrai pas la foule du peuple qui m'assiège de tous côtés;
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 Lève-toi, Seigneur; sauve-moi, mon Dieu! Car tu as frappé tous ceux qui m'ont poursuivi sans cause, et tu as broyé les dents des pécheurs.
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Le salut vient du Seigneur, et ta bénédiction est sur ton peuple.
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Psaumes 3 >