< Psaumes 25 >
1 Psaume de David. Vers toi, Seigneur, j'ai élevé mon âme.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 O mon Dieu, je me suis confié en toi: que je ne sois pas confondu! Que mes ennemis ne se moquent point de moi;
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Car nul de ceux qui t'attendent ne sera confondu. Soient confondus tous ceux qui, dans leur vanité, agissent contre la justice.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Montre-moi tes voies, fais-moi connaître tes sentiers.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Conduis-moi dans ta vérité, et instruis-moi; car tu es, ô Dieu, mon Sauveur, et je t'ai attendu tout le jour.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Seigneur, souviens-toi de ta compassion et de tes miséricordes; car tes miséricordes sont de toute éternité.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Ne te rappelle pas les péchés de ma jeunesse ni mes inadvertances; Seigneur, souviens-toi de moi en ta miséricorde, et à cause de ta bonté.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Le Seigneur est doux, il est droit; aussi, par sa loi, il remettra dans la voie les pécheurs.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Il guidera les doux dans la justice; il enseignera ses voies aux doux.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Toutes les voies du Seigneur sont miséricorde et vérité, pour ceux qui cherchent son alliance et ses témoignages.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 Pour l'amour de ton nom, Seigneur, tu me pardonneras mon péché, parce qu'il est grand.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Quel est l'homme qui craint le Seigneur? Le Seigneur lui prescrira une loi dans la voie que lui-même a choisie.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 Son âme résidera au milieu des biens, et sa race héritera de toute la terre.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 Le Seigneur est la force de ceux qui le craignent, [et le nom du Seigneur est pour ceux qui le craignent], et son alliance existe pour leur être montrée.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mes yeux seront toujours tournés vers le Seigneur, parce que lui-même retirera mes pieds des filets.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Regarde-moi et aie pitié de moi, car je suis seul et pauvre.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Les afflictions de mon cœur se sont multipliées; délivre-moi de ma détresse.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Vois mon humiliation et ma douleur, et remets-moi tous mes péchés.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Vois mes ennemis, comme ils se sont multipliés, et comme ils m'ont haï d'une haine injuste.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Garde mon âme et délivre-moi; que je ne sois point confondu, car j'ai espéré en toi.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Les innocents et les cœurs droits me sont attachés, Seigneur, parce que je t'ai attendu.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 O mon Dieu, délivre Israël de toutes ses afflictions.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!