< Psaumes 137 >

1 De David. Sur les fleuves de Babylone nous nous sommes assis, et nous avons pleuré, en nous souvenant de Sion.
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 Nous avons suspendu nos harpes aux saules, qui sont au milieu de la contrée.
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 Car ceux qui nous avaient faits captifs nous demandaient les paroles de nos cantiques; et ceux qui nous avaient emmenés nous disaient: Chantez-nous un hymne des cantiques de Sion!
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 Comment chanterons-nous un cantique du Seigneur sur une terre étrangère?
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 Si je t'oublie, Jérusalem, que ma main droite s'oublie elle-même!
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Si je ne me propose Jérusalem comme le principe de mes joies; si je ne me souviens point de toi, que ma langue s'attache à mon gosier.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Souviens-toi, Seigneur, des fils d'Édom, qui, au dernier jour de Jérusalem, disaient; Détruisez-la, détruisez-la jusqu'en ses fondements!
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 Fille de Babylone, infortunée! heureux celui qui te rendra le mal en retour du mal que tu as fait!
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 Heureux celui qui saisira tes petits enfants et les écrasera contre la pierre!
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psaumes 137 >