< Psaumes 135 >
1 Alléluiah! Louez le Seigneur, ô vous qui êtes ses serviteurs; louez le Seigneur!
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Vous qui vous tenez en sa maison, dans les parvis de la maison de notre Dieu,
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Louez le Seigneur, parce que le Seigneur est bon; chantez des psaumes à son nom, parce que son nom est beau.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Car le Seigneur a choisi Jacob pour être à lui Jacob, et Israël pour être sa possession.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Et moi j'ai reconnu que le Seigneur est grand, que notre Dieu est au- dessus de tous les dieux.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Tout ce que le Seigneur a voulu, il l'a fait; dans le ciel et sur la terre, et dans la mer, et dans tous les abîmes.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Il amène les nuées des extrémités de la terre; il change les éclairs en pluie. C'est lui qui tire les vents de ses trésors.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 C'est lui qui a frappé les premiers-nés d'Egypte, depuis l'homme jusqu'aux troupeaux;
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 Lui qui a envoyé ses signes et ses prodiges au milieu de toi, Egypte, devant le Pharaon et tous ses serviteurs;
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Lui qui a frappé maintes nations et tué des rois puissants:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Séhon, roi des Amorrhéens et Og, roi de Basan, et tous les rois chananéens;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 Et qui a donné leur héritage en héritage à Israël, son peuple.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Seigneur, ton nom est éternel, et ta mémoire passe de génération en génération.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Car le Seigneur jugera son peuple, et il écoutera les prières de ses serviteurs.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Les idoles des Gentils sont argent et or, œuvres des mains des hommes.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Elles ont une bouche, et ne parleront pas; elles ont des yeux, et ne verront pas.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Elles ont des oreilles, et n'entendront pas [des narines, et ne sentent pas, des mains et ne touchent pas, des pieds et ne marchent pas, et il n'y a pas de voix dans leur gosier]; et il n'est point de souffle en leur bouche.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Que ceux qui les font leur deviennent semblables, et tous ceux qui croient en elles.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Maison d'Israël, bénis le Seigneur; maison d'Aaron, bénis le Seigneur.
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Maison de Lévi, bénis le Seigneur; vous qui craignez le Seigneur, bénissez le Seigneur.
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Béni soit le Seigneur en Sion, lui qui habite Jérusalem!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.