< Psaumes 115 >
1 Non pas à nous, Seigneur, non pas à nous, mais à ton nom, donnez-en la gloire,
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 A cause de ta miséricorde et de ta vérité; de peur que les Gentils ne viennent à dire: Où est leur Dieu?
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Notre Dieu est dans le ciel et sur la terre; tout ce qu'il a voulu, il l'a fait.
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 Les idoles des Gentils sont argent et or, œuvres de la main des hommes.
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 Elles ont une bouche, et ne parleront pas; elles ont des yeux, et ne verront pas.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 Elles ont des oreilles, et n'entendront pas; elles ont des narines, et ne sentiront pas.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 Elles ont des mains, et ne toucheront pas; elles ont des pieds, et ne marcheront pas, et nul cri ne sortira de leur gosier.
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 Que ceux qui les font leur deviennent semblables, et tous ceux qui croient en elles.
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 La maison d'Israël a espéré dans le Seigneur, il est son champion et son appui.
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 La maison d'Aaron a espéré dans le Seigneur, il est son champion et son appui.
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 Ceux qui craignent le Seigneur ont espéré dans le Seigneur; il est leur champion et leur appui.
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 Le Seigneur s'est souvenu de nous, et nous a bénis; il a béni la maison d'Israël, il a béni la maison d'Aaron.
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 Il a béni ceux qui craignent le Seigneur, les petits aussi bien que les grands.
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 Que le Seigneur fasse plus encore pour vous, pour vous et pour vos enfants.
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 Soyez bénis du Seigneur, qui a fait le ciel et la terre.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 Le ciel des cieux est au Seigneur; mais la terre il l'a donnée aux fils des hommes.
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 Les morts, Seigneur, ne te loueront point ni tous ceux qui descendent en enfer. ()
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 Mais nous qui vivons, nous bénirons le Seigneur, maintenant, et dans tous les siècles.
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.