< Psaumes 110 >

1 Psaume de David. Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Assieds-toi à ma droite, jusqu'à ce que j'aie fait de tes ennemis l'escabeau de tes pieds.
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 Le Seigneur t'enverra de Sion le sceptre de ta puissance; règne au milieu de tes ennemis.
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Le principe est avec toi au jour de ta puissance, parmi les splendeurs de tes saints. Je t'ai engendré de mes entrailles, avant l'étoile du matin.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 Le Seigneur l'a juré, et il ne s'en repentira pas: tu es le prêtre éternel, selon l'ordre de Melchisédech.
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 Le Seigneur est à ta droite; il a écrasé les rois le jour de sa colère.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 Il jugera au milieu des nations; il les remplira de ruines; il brisera sur la terre la tête d'une grande multitude.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 Il boira sur son chemin l'eau du torrent, et, à cause de cela, il relèvera sa tête.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.

< Psaumes 110 >