< Psaumes 107 >

1 Alléluiah! Rendez gloire au Seigneur, parce qu'il est bon, parce que sa miséricorde est éternelle.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qu'ainsi disent ceux qui ont été rachetés par le Seigneur, qu'il a délivrés de la main de leurs ennemis et rassemblés des contrées
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Du levant et du couchant, de la mer et de l'aquilon.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ils ont erré dans le désert sans eau; ils n'y ont point trouvé le chemin d'une cité habitable,
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Et ils avaient faim, ils avaient soif; et leur âme était défaillante.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Et, dans leur tribulation, ils crièrent au Seigneur, et il les retira de leur détresse.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Et il les conduisit dans le droit chemin, afin qu'ils arrivassent à une cité habitable.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Qu'ils rendent gloire à la miséricorde du Seigneur et à ses prodiges en faveur des fils des hommes;
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Car il a rassasié leur âme vide, et rempli de biens leur âme affamée.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Assis dans les ténèbres et à l'ombre de la mort, ils étaient enchaînés par la pauvreté et le fer;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Parce qu'ils avaient provoqué les voix du Seigneur, et avaient irrité le conseil du Très-Haut.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Et leur cœur fut humilié dans leurs labeurs, et ils furent sans force, et nul n'était là pour les secourir.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Et dans leurs tribulations ils crièrent au Seigneur, et il les retira de leur détresse.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Et il les tira des ténèbres et de l'ombre de la mort, et brisa leurs chaînes.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Qu'ils rendent gloire au Seigneur de sa miséricorde et de ses prodiges en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Car il a fait voler en éclats les portes d'airain; il a brisé les verrous de fer.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Il les a aidés à sortir de la voie de leur iniquité; et, à cause de leurs infidélités, ils avaient été humiliés.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Leur âme avait pris en abomination tout aliment, et déjà ils étaient près des portes de la mort.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Et dans leurs tribulations ils crièrent au Seigneur, et il les sauva de leur détresse.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Et il envoya sa parole, et il les a guéris, et il les arrachés de leur perdition.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Qu'ils rendent gloire au Seigneur de sa miséricorde et de ses prodiges en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Et qu'ils lui offrent des oblations de louanges, et qu'ils annoncent ses œuvres avec des transports d'allégresse.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ceux qui voguent sur la mer dans leurs barques, et qui trafiquent au milieu des eaux,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ceux-là ont vu les œuvres du Seigneur, et ses merveilles dans l'abîme.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Il dit, et le vent impétueux de la tempête s'est levé, et les vagues ont bondi.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Elles montent jusqu'aux cieux et descendent jusqu'aux abîmes, et l'âme des matelots succombe à la violence du mal.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Ils sont troublés, ils chancellent comme des hommes ivres, et toute leur sagesse a été engloutie.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Et dans leur tribulation ils ont crié au Seigneur, et il les a retirés de leur détresse.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Et il a commandé à la tempête, et elle s'est changée en une brise légère, et les flots ont fait silence.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Et les hommes se sont réjouis de leur calme, et le Seigneur les a conduits au port désiré.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Qu'ils rendent gloire au Seigneur de sa miséricorde et de ses prodiges en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Qu'ils l'exaltent dans l'assemblée du peuple, et le louent sur le siège des anciens.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Il a changé des fleuves en un désert, et des eaux jaillissantes en une terre altérée;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Et une terre fertile en un lieu saumâtre, à cause de la malice de ceux qui l'habitaient.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Il a fait d'un désert un étang plein d'eau, et d'une terre sans eau des vallons arrosés.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Et il y a mis des affamés, et ils ont bâti des cités habitables.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Et ils ont ensemencé des champs, et ils ont planté des vignes, et ils en ont récolté les produits.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Et il les a bénis, et ils se sont prodigieusement multipliés, et il n'a pas amoindri le nombre de leur bétail.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Puis ils ont déchu, et ils ont été maltraités par les tribulations, les maux et la douleur.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Et le mépris s'est répandu sur leurs princes, et Dieu les a laissés s'égarer en des lieux impraticables et sans voie.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Et il a délivré le pauvre de sa misère, et il a traité sa famille comme des brebis.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Les justes le verront et en seront réjouis, et toute iniquité fermera sa bouche.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Quel est le sage qui gardera ces choses, et comprendra les miséricordes du Seigneur?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psaumes 107 >