< Psaumes 105 >

1 Alléluiah! Rendez grâces au Seigneur, et invoquez son nom; annoncez ses œuvres parmi les Gentils.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Chantez en son honneur, chantez-lui des psaumes; racontez toutes ses merveilles.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glorifiez-vous en son saint nom; que le cœur de ceux qui cherchent le Seigneur soit réjoui.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Cherchez le Seigneur, et soyez forts; cherchez perpétuellement sa face.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Souvenez -vous des prodiges qu'il a faits, de ses merveilles et des jugements de sa bouche.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Enfants d'Abraham, qui êtes ses serviteurs, fils de Jacob, qui êtes ses élus,
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Le Seigneur est notre Dieu; ses jugements sont sur toute la terre.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Il s'est souvenu pour toujours de son alliance, de la parole qu'il a intimée à des milliers de générations,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Et qu'il a conclue avec Abraham; il s'est souvenu de son serment à Isaac.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 Et cette alliance avec Jacob, il l'a érigée en commandement; et avec Israël, en testament éternel,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Disant: Je te donnerai la terre de Chanaan, comme part de votre héritage.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Ils y étaient alors en petit nombre, et passagers en cette terre.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Et ils allèrent d'une nation à une autre, et d'un royaume à un autre peuple.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Et à nul homme Dieu ne permit de leur faire tort, et, à cause d'eux, il châtiait les rois, disant:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Gardez-vous de toucher à mes oints; gardez-vous de maltraiter mes prophètes.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Et il appela la famine sur la terre, et il brisa la force que donnait le pain.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Et il envoya un homme devant eux, et Joseph fut vendu comme esclave.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Ils l'humilièrent, en mettant à ses pieds des entraves; et le fer traversa son âme.
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Mais quand lui vint la parole du Seigneur, cette voix l'enflamma.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Le roi, prince des peuples, envoya des hommes pour le délier, et il le mit en liberté,
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Et il le constitua maître de sa maison et prince de ses richesses,
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Pour qu'il instruisît les grands comme lui-même, et enseignât la sagesse à ses anciens.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Et Israël entra en Egypte, et Jacob habita en la terre de Cham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Et Dieu multiplia extrêmement son peuple; et il l'affermit contre ses ennemis.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Puis il changea le cœur de ceux-ci, afin qu'ils haïssent son peuple et usassent de fraude contre ses serviteurs.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Et il envoya Moïse son serviteur, et Aaron, son élu.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Il mit en eux les paroles de ses signes et de ses prodiges en la terre de Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Il envoya les ténèbres et l'obscurité; et ils s'irritèrent de ses paroles,
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Il changea leurs eaux en sang, et il fit mourir leurs poissons.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Leur terre produisit des grenouilles, jusqu'aux chambres les plus retirées des princes.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Il dit, et des mouches de chien et des moucherons vinrent dans toute leur contrée.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Il fit tourner leur pluie en grêle, et le feu dévora leur terre.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Et il frappa leurs vignes et leurs figuiers, et brisa tous les arbres sur leur territoire.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Il dit, et des sauterelles et des chenilles vinrent en quantité innombrable;
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 Et elles rongèrent toute l'herbe de la terre et en mangèrent tous les fruits.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Et il frappa tout premier-né de leur terre, prélude de toutes leurs peines.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Et il fit sortir les Hébreux avec de l'argent et de l'or, et parmi leurs tribus il n'y avait pas un infirme.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 L'Egypte se réjouit de leur départ, parce que la crainte qu'elle avait d'eux était retombée sur elle.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Le Seigneur étendit une nuée pour les couvrir, et un feu pour les éclairer la nuit.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Ils demandèrent, et des cailles vinrent; et il les rassasia d'un pain venu du ciel.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Il fendit le rocher, et les eaux jaillirent; des fleuves coulèrent sur une terre aride,
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Parce que le Seigneur se souvint de sa parole sainte, qu'il avait donnée à Abraham, son serviteur;
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Et il délivra son peuple dans l'allégresse, et ses élus dans la joie.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 Et il leur donna les régions des Gentils, et ils héritèrent des travaux des peuples;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Afin qu'ils gardassent ses commandements, et recherchassent sa loi.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psaumes 105 >